Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai Afrika
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari Afrika
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe Afrika
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS Afrika
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe Afrika

A Kowacce Rana Kasar China Tana Sayan Danyen Mai Ganga Dubu 600 Daga Kasar Venezuela
Published: December 18, 2025 at 8:25 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Kasar China ta ce tana adawa da matakin nuna fin karfi, bayan Amurka ta bada umurnin tare dukkan jiragen ruwan jigilar mai da aka kafa ma takunkumi wadanda ke kokarin zuwa ko fitowa daga kasar venezuela mai arzikin man fetur.

China ita ce ta fi kowace kasa sayen danyen man kasar Venezuela, inda a wannan watan ake sa ran cewa a kowace rana zata na saye ganga dubu 600 na man Venezuela.

Ministan harkokin wajen China, Wang Yi, ya fadawa takwaransa na Venezuela a tattaunawar da suka yi ta wayar tarho cewa China tana yin adawa da duk wani matakin nuna fin karfi da wata kasa zata so nunawa, sannan tana goyon bayan kasashe wajen kare mutuncin kasarsu.

Wang bai ambaci sunan Amurka ko shugaba Trump a bayanin da aka bayar na tattaunawar ba, haka kuma bai fadi irin tallafin da China zata iya ba Venezuela ba.

Shugaba Nicolas Maduro yace Amurka tana neman mallakar danyen man fetur na Venezuela ne, kuma girke sojojin da take yi a yankin na neman hambarar da shi daga kan mulki ne.

Amurka dai ta ce tana yakar safarar muggan kwayoyi ne zuwa cikin kasarta.

Amurka

Post navigation

Previous Post: Kotun Kasar Rasha Ta Daure Dan Kasar Belarus Shekarar 22 A Kurkuku
Next Post: Boko Haram Sun Dauke Kansiloli A Borno

Karin Labarai Masu Alaka

‘Yan Sanda A Tsibirin Bahamas Sun kama Mijin Wata Ba Amurkiya Amurka
Rundunar Sojin Amurka Sunfara Ficewa Daga Kasar Sham Amurka
Sojojin Amurka Sun Kashe Wasu Fararen Hula Ba Dalili Amurka
Amurka Ta Cire Takunkumin Da Ta Kakabawa Shugaban Venezuela Amurka
Shugaba Trump Ya Amince Da Tsawaita Cinikayya Tsakanin Amurka Da Kasashen Afirka Afrika
Kasar Canada Ta Amince A Shigar Da Motoci Kirar Kasar China Kasar Amurka

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Messi Da Cristiano Suna Da Tasiri A Gasar Cin Kofin Duniya 2026 Wasanni
  • Hatsarin Mota Yayi Ajalin Mutum 7 A Gombe Najeriya
  • ‘Yan Uwa Musulmi A Jihar Gombe Sunyi Allah Wadai Da Kisan Ayatollah Khomeini Afrika
  • Shugaba Tinubu Ya Ayyana Dokar-Ta-Baci A Fannin Tsaro Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Karancin Iskar Gas Kalubale Ne Ga Wutar Lantarki Labarai
  • Bankin Duniya Zaibawa Kasar Mozambique Lamunin Dala Bilyan Shida Labarai
  • Najeriya Da Amurka Sun Karfafa Alakar Tsaro Afrika
  • Kotun Kasar Rasha Ta Daure Dan Kasar Belarus Shekarar 22 A Kurkuku Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.