Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe Afrika
  • Hukumomin Bada Agaji Sun Fadakar Da Al’ummar Jihar Gombe Afrika
  • Ana Cigaba Da Shirye-Shiryen Fara Gasar Kwallon Sarakuna A Gombe Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Zata Samar Da Sabbin Dakunan Karatun Dalibai Afrika
  • Gwamnatin Tarayya Ta Cire Sharadin Rubuta UTME Ga Masu Neman Shiga Kwalejojin Ilimi Afrika

Dakarun Tsaron Ruwan Amurka Sunfara Killace Hanyoyi
Published: April 14, 2026 at 8:19 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Dakarun Amurka ta ruwa a ranar Litinin suka fara killace hanyoyin ruwa na kasar Iran, tare da hana jiragen ruwa shiga ko fita daga tashoshin ruwa na kasar, inji shugaba Donald Trump, Iran tayi barazanar zata rama kan kasashe makwabta a yankin Gulf, bayanda aka tashi baram baram a shawarwari da suka yi a Pakistan, da nufin kawo karshen yakin da suke gwabzawa.

Wani jami’in Amurka yace ana ci gaba da tuntubar juna da Iran, da nufin cimma yarjejeniya. Shi ma Prime Ministan Pakistan Shehbaz Sharif yace ana ci gaba da kokarin warware rikicin.

Saboda wannan yanayi da ake ciki, farashin mai ya sake cullawa sama da dala dari kan ko wace ganga, ba tare da an ga wata alamar za’a bude mashigin ruwa na Hormuz nan take ba, domin sassauta kassara jigilar mai mafi girma a tarihi, da kuma ci gaba da nuna damuwa kan dorewar yarjejeniyar tsagaita wuta na mako biyu da aka cimma cikin makon jiya.

Trump ya fada a jiya Litnin cewa Iran ta yi tuntuba a jiyan tana son a kulla yarjejeniya, amma ba zai amince da duk wata yarjejeniyar da zata kyale Iran ta mallaki makaman Nukiliya ba.

Tun bayan da Amurka da Isra’ila suka kaddamar da hare hare akan Iran ranar 28 ga watan Febwairu, Iran ta rufe mashigin ruwa na Hormuz ga dukkan jiragen ruwa in banda nata, tana mai cewa ba jirgin ruwan da za’a kyale ya wuce ba tare da izininta ba tare da an biyan wani hasafi.

Trump yace Washington zata hana duk wani jirgin ruwa daga Iran, da duka jiragen da suka biya Farisa wani kudi wuce wa, kuma duk wani karamin jirgin ruwan Iran masu kai hari da ya yi kusa da jiragen ruwa yaki na Amurka zai zama tarihi.

Amurka, Labarai, Sauran Duniya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Tsohon Jagoran Masu Kishin Kasa A Hungry Ya Amince Da Shan Kaye
Next Post: Kawayen Amurka Bazasu Shiga Matakin Shugaba Trump Ba

Karin Labarai Masu Alaka

‘Yan Sanda Sunce Mutum Daya Ne Yakai Hare-Haren Jami’ar Brown Da Kuma Na MIT Boston Amurka
Rundunar Sojin Amurka Zasu Kaiwa Iran Hari Amurka
Ruwa Kamar Da Bakin Kwarya Ya Haifar Da Mutuwar Mutane A Nairobi Afrika
Babban Hafsan Tsaron Najeriya Ya Gargadi Masu Tayar Da Hankali Najeriya
Farashin Kasuwar Yawon Bude Ido A Kasuwar Hannayen Jari Ya Fadi Afrika
Trump: Isra’ila Ta Daina Kai Hari Ga Duk Cibiyar Iskar Gas Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe
  • Hukumomin Bada Agaji Sun Fadakar Da Al’ummar Jihar Gombe
  • Ana Cigaba Da Shirye-Shiryen Fara Gasar Kwallon Sarakuna A Gombe
  • Gwamnatin Najeriya Zata Samar Da Sabbin Dakunan Karatun Dalibai
  • Gwamnatin Tarayya Ta Cire Sharadin Rubuta UTME Ga Masu Neman Shiga Kwalejojin Ilimi

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Dubban ‘Yan Gudun Hijira Sun Halaka Amurka
  • Shugaba Bola Tinubu Ya Tafi Turai Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Jami’ar ABU Zaria Ta Karbi Kudade Naira Bilyan 1.3 Daga Shirin Nelfund Afrika
  • Nigeria Zata Bude Asusun Dala Bilyan Biyu Don Habaka Sashin Makamashi Labarai
  • Makiyaya Sun Shiga Matsala Sakamakon Fari A Kasar Kenya Afrika
  • Shugaba Tinubu ya mika sunayen Sabbin Shugabannin NMDPRA da NUPRC Bayan Murabus Din Farouk Ahmad Da Gbenga Komolafe Najeriya
  • Shugaba Tinubu Yace Bazai Bawa ‘Yan Najeriya Kunya Ba Afrika
  • Kimanin Mutane 200 Ne Suka A Mutu A Wani Harin Jirgin Yakin Sojin Najeriya Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.