Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

Shugaban Kasar Ghana Ya Soki Manufofin Gwamnatin Amurka
Published: March 25, 2026 at 4:34 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Ranar talata a New York, shugaban kasar Ghana, John Daramani Mahama, ya soki manufofin gwamnatin Amurka, kan abunda ya kira amincewa da goge tarihin bakar fata, yana mai cewa hakan zai iya shafar wasu lamura sosai.

Tun bayan da ya dawo kan madafun iko, shugaba Donald Trump, ya auna hukumomi da cibiyoyin al’adun gargajiya, da suka hada da wuraren adana tarihi da wasu kayan al’adu, domin cire abunda ya kira “manufofin nuna kiyayya ga Amurka.”

Kalaman shugaba Trump da wasu dokokin shugaban kasa, da ake kira Executive orders, sun kai ga cire wasu kayan tarihin bautar da bakar fata, sake dawo da kayan tarihin turawa masu da’awar wariya, da wasu matakai da masu yakin tabbatar da ‘yancin tsiraru suke ganin zai maida hanun agogo baya.

Wadan nan matakai sun zama manhaja ga wasu gwamnatoci da kungiyoyi ko kamfanoni masu zaman kansu,” inji shugaba John Daramani, lokacin da yake magana a wani lamari a MDD, yace ko babu komi sannu a hankali matakan suna halatta goge tarihi.

Shugaba Mahama yace a Amurka ana cire kososhi da suke koyar da tarihin bakar fata a makarantu, ana tilastawa cibiyoyi su daina koyarda “gaskiyar tarhin bauta da wariyar launin fata,” kuma littatafai da suke karantar da wannan batu ana ci gaba da haramta su.

Shugaba Mahama a bara, ya amince da wani shirin karbar ‘yan asalin Afirka ta yamma da gwamnatin Trump ta tusa keyar su, a baya ya soki shugaba Trump kan karyar da yayi cewa ana yiwa turawa kisan kare dangi tare da kwache musu filaye a Afirka ta kudu, da cewa fadin hakan cin fuska ne ga daukacin Afirka.

Fadar White House bata maida martani nan take kan maganar shugaba John Daramani Mahama.

Afrika, Amurka, Labarai, Siyasa

Post navigation

Previous Post: Dillalan Mai Suna Fuskantar Karancin Mai Sakamakon Yakin Amurka Da Iran
Next Post: Hukumar MDD Tace Wadanda Suka Mutu A Harin Sudan Sun Haura 70

Karin Labarai Masu Alaka

Shugaba Trump Ya Janye Karbar Kudin Fito Daga Wasu Kasashen Turai Amurka
Samar Da Albarkatun Mai Ya Ragu A Iraq Afrika
Jagoran Kwankwasiya A Najeriya Ya Koma Jam’iyar ADC Labarai
Kotun Daukaka Kara A Faransa Zata Tabbatar Da Hukuncin ‘Yan Jam’iyyar Ra’ayin Rikau Labarai
Amurka Ta Kama Tsohon Ministan Kudin Kasar Ghana Afrika
Amurka Zata Bawa Ukraine Tsaro Na Musamman Amurka

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Mayakan M23 Sun Tsagaita Wuta A Gabashin Kwango Labarai
  • Sojojin Amurka Sun Isa Najeriya Don Yaki Da Ta’addanci Amurka
  • ‘Yan Sandan Bauchi Sun Kama Mutum Biyu Kan Zargin Fashi da Makami A Gadau Afrika
  • Nada Jakadu Da Tinubu Yayi Sako Ne Ga ‘Yan-Arewa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Tinubu Ya Maye Gurbin Badaru Da Tsohon Soja Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Sojojin Najeriya Sun Kashe Fitaccen ’Yan Bindiga Kallamu A Jihar Sakkwato Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ruwa Kamar Da Bakin Kwarya Ya Haifar Da Mutuwar Mutane A Nairobi Afrika
  • Kamfanin Bitcoin A Korea Ta Kudu Yayi Kuskuren Turawa Masu Mu’amala Da Kamfanin Kudade Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.