Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe Afrika
  • Hukumomin Bada Agaji Sun Fadakar Da Al’ummar Jihar Gombe Afrika
  • Ana Cigaba Da Shirye-Shiryen Fara Gasar Kwallon Sarakuna A Gombe Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Zata Samar Da Sabbin Dakunan Karatun Dalibai Afrika
  • Gwamnatin Tarayya Ta Cire Sharadin Rubuta UTME Ga Masu Neman Shiga Kwalejojin Ilimi Afrika

Shugaban Kasar Ghana Ya Soki Manufofin Gwamnatin Amurka
Published: March 25, 2026 at 4:34 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Ranar talata a New York, shugaban kasar Ghana, John Daramani Mahama, ya soki manufofin gwamnatin Amurka, kan abunda ya kira amincewa da goge tarihin bakar fata, yana mai cewa hakan zai iya shafar wasu lamura sosai.

Tun bayan da ya dawo kan madafun iko, shugaba Donald Trump, ya auna hukumomi da cibiyoyin al’adun gargajiya, da suka hada da wuraren adana tarihi da wasu kayan al’adu, domin cire abunda ya kira “manufofin nuna kiyayya ga Amurka.”

Kalaman shugaba Trump da wasu dokokin shugaban kasa, da ake kira Executive orders, sun kai ga cire wasu kayan tarihin bautar da bakar fata, sake dawo da kayan tarihin turawa masu da’awar wariya, da wasu matakai da masu yakin tabbatar da ‘yancin tsiraru suke ganin zai maida hanun agogo baya.

Wadan nan matakai sun zama manhaja ga wasu gwamnatoci da kungiyoyi ko kamfanoni masu zaman kansu,” inji shugaba John Daramani, lokacin da yake magana a wani lamari a MDD, yace ko babu komi sannu a hankali matakan suna halatta goge tarihi.

Shugaba Mahama yace a Amurka ana cire kososhi da suke koyar da tarihin bakar fata a makarantu, ana tilastawa cibiyoyi su daina koyarda “gaskiyar tarhin bauta da wariyar launin fata,” kuma littatafai da suke karantar da wannan batu ana ci gaba da haramta su.

Shugaba Mahama a bara, ya amince da wani shirin karbar ‘yan asalin Afirka ta yamma da gwamnatin Trump ta tusa keyar su, a baya ya soki shugaba Trump kan karyar da yayi cewa ana yiwa turawa kisan kare dangi tare da kwache musu filaye a Afirka ta kudu, da cewa fadin hakan cin fuska ne ga daukacin Afirka.

Fadar White House bata maida martani nan take kan maganar shugaba John Daramani Mahama.

Afrika, Amurka, Labarai, Siyasa

Post navigation

Previous Post: Dillalan Mai Suna Fuskantar Karancin Mai Sakamakon Yakin Amurka Da Iran
Next Post: Hukumar MDD Tace Wadanda Suka Mutu A Harin Sudan Sun Haura 70

Karin Labarai Masu Alaka

Iran Zata Kawo Karshen Yaki Da Isra’ila Da Amurka Amurka
An Tura Rundunar Tsaron Sham Zuwa Kakarshin Ikon Kurdawa Labarai
Hukumar MDD Tace Wadanda Suka Mutu A Harin Sudan Sun Haura 70 Afrika
Mutane Da Dama Sun Rasa Rayukansu Yayin Rikici A Uganda Siyasa
Muna Kokarin Kawo Karshen Cin Zarafin Jinsi A Gombe – Uwargidan Gwamna Labarai
Jamhuriyar Congo Zata Cigaba Da Fitar Da Ma’adanai Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe
  • Hukumomin Bada Agaji Sun Fadakar Da Al’ummar Jihar Gombe
  • Ana Cigaba Da Shirye-Shiryen Fara Gasar Kwallon Sarakuna A Gombe
  • Gwamnatin Najeriya Zata Samar Da Sabbin Dakunan Karatun Dalibai
  • Gwamnatin Tarayya Ta Cire Sharadin Rubuta UTME Ga Masu Neman Shiga Kwalejojin Ilimi

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Wani Harin ‘Yan Bindiga Ya Kashe Mutane 35 A Jihar Borno Labarai
  • Iran Ta Kai Hari Matatar Mai A Kuwait Afrika
  • Taron Masu Mu’amala Da Kafar Facebook A Kano Afrika
  • ‘Yan Bindiga Sun Hallaka Mutane 30 A Jihar Neja Najeriya
  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Sojoji A Jihar Kebbi Afrika
  • An Gudanar Da Jana’izar ’Yan Jaridan Da Suka Rasu A Jihar Gombe Labarai
  • Fargaba Ta Karu Duk Da Tsagaita Wuta Tsakanin Iran Da Amurka Afrika
  • Kanal Sani: Idan ‘Yan-Ta’adda Zasu Mutunta Sulhu To Gwamnati Ta Duba Hakan Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.