Hukumar kiwon lafiya ta MDD tace yawan wadanda suka halaka Sakamakon harin da aka kai kan wani asibiti da jirgin yaki da bashi da matuki a Sudan ya haura zuwa 70, adadin da ya hada da mata da yara, da masu aikin kiwon lafiya, saboda an sami karin gawarwarki da ake zakulowa karkashin baraguzai.
An kaiwa asibitin koyarwa na al-Deain da yake gabashin Darfur hari ranar 20 ga watan Maris da muke ciki, inji hukumar ba tare da ta aza laifi ba. Hukumar Lafiya ta Duniya WHO, tace dama asibitin shine yake zaman cibiya da yake duba mutane sama da da milyan biyu, yanzu ya daina aiki.


