Gwamnatin kasar Ghana na shirin sauya shekar inda take aikewa da gwal dinta don sarrafa shi, idan aka ci gaba da samun tsaiko wajen tashin jiragen sama zuwa Hadaddiyar Daular Larabawa, a cewar wasu majiyoyi biyu dake da masaniya kan abun, yayin da rikicin Iran ya bankado yadda Afirka take dogaro da Dubai a harkar gwal.
Ana aikewa da gwal kai tsaye zuwa Dubai, wadda babbar kasuwa ce dake cinikar da gwal din ga kasashen Switzerland, Honk Kong, da kuma India. Yau kwanaki 7 kenan da samun tsaiko wajen aika gwal din a dalilin harin da Amurka da Isra’ila suka kaiwa Iran, da ita kuma Iran din ta kai harin kan sansanin sojin Amurka a Gabas ta tsakiya, abinda ya jawo rufe tasoshin jiragen sama a Dubai.
Ita kuma Ghana, wadda ita ce kasar da tafi samar da gwal a Afirka, kuma ta 6 a duniya, Dubai ce ke sarrafa kusan kashi 80 cikin 100 na gwal din ta. Amma saboda yakin da ake tafkawa, ya rufe hanyar Dubai, Ghana ta shirya tsarin kai gwal din zuwa China ko India don sarrafawa.


