‘Yan bindiga sun hallaka sojoji 15, suka kuma jikkata wasu 5 a wani sansanin soji a arewacin Jamhuriyar Benin, a cewar wani mai magana da yawun sojojin a ranar Jumu’a.
‘Yan bindiga dake da alaqa da kungiyar ‘yan ta’adda ta Al-Qa’idah da ISIS, suna kara kai hare-hare iyakokin kasashen Niger, Benin da Nigeria, inda suka mai da yankin kamar wani sansanin yaki.
Kungiyar Jamat Nusrat al Islam dake da alaqa da al-Qaidah ta dau alhakin kai harin na Benin, wanda ta ce ya faru ne a arewacin kauyen Kofouno ranar Laraba.


