Akalla Mutane 37 ne aka kashe ta hanyar yi masu yankan rago a Jihar Nejan Najeriya.
Rahotanni daga kauyen kasuwar Daji dake yankin karamar Hukumar Borgu na nuna cewa wasu mahara da ake zaton mayakan lakurawa ne ko kuma Boko Haram bayan kashe wadan nan mutane sun kuma yi garkuwa da wasu mutanen da dama.
Wasu daga cikin mazauna yankin sunce maharan sun share yinin ranar Asabar suna ta’asubancinsu a yankin tare da kona kasuwar Garin.
Shugaban karamar hukumar ta Borgu Hon. Muhammad Nasir Abdullahi ya tabbatar da aukuwar lamarin inda yace suna cikin yanayi na tashin hankali.
Gwamnatin jihar Nejan tace tana cikin yanayi na tashin hankali amma kuma Gwamnati na daukar mataki na shawo kan wannan matsala a ta bakin Hon. Obed Nana Kwamishina yada Labarai na Jihar Nejan, ya kara da cewa sun hada hannu da Gwamnatin Tarayya domin tun karar matsalar kai tsaye.
Yankin na kasuwar Daji dai yana kusa da Garin Papiri inda aka saci yaran makarantar St Mary a cikin watan Nuwamban da ta gabata.


