Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • PDP Ta Tsayar da Goodluck Jonathan Takarar Shugaban Kasa Afrika
  • Hawan Gidan Gwamnati A Jihar Gombe Afrika
  • Hawan Babbar Sallah A Masarautar Kaltungo Dake Jihar Gombe Afrika
  • Sarkin Gombe Ya Yabi Nasarorin Inuwa Yahaya A Fannonin Tsaro Da Raya Kasa Afrika
  • Tinubu Ya Jaddada Aniyar Rage Tsadar Rayuwa Da Samar da Ayyukan Yi Afrika

Hukumar Zabe A Najeriya Ta Cigaba Da Rijistar Katin Zabe
Published: January 5, 2026 at 6:16 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Hukumar zaɓe mai zaman kanta ta Najeriya wato (INEC) ta sake dawo da yin rajistar masu zaɓe na dindindin a faɗin Najeriya, inda hakan ke nuna fara zango na biyu na aikin.

INEC ta ce an dawo da aikin ne bayan kammala zangon farko da ya ƙare a ranar 10 ga Disamba, 2025.

Hukumar takara da cewa, sama da ’yan Najeriya miliyan 9.8 ne suka fara rajistar yanar gizo a zangon farko, yayin da kusan miliyan 2.57 ne aka kammala musu Rijistar gaba ɗaya.

Hukumar ta bayyana cewa an yi amfani da tazara tsakanin zango na biyu wajen gudanar da ayyukan doka, ciki har da nuna kundin masu zaɓe domin karɓar ƙorafe-ƙorafe da ƙin amincewa.

INEC ta buƙaci ’yan Najeriya da suka cancanta su yi amfani da damar da aka samu wajen yin rajista, sauya wurin zaɓe ko sabunta bayanansu, haka kuma ta nemi waɗanda suka yi rajista a zangon farko su ci gaba da tantance bayanansu tare da kai rahoton duk wani kuskure.

Sai dai hukumar ta ce har yanzu an dakatar da rajistar masu zaɓe a jihar Anambra da Abuja sakamakon ci gaba da harkokin zaɓe, inda ta ƙara da cewa za a sanar da sabbin ranakun sake farawa nan gaba.

Labarai

Post navigation

Previous Post: ‘Yan-Ta’adda Sun Yi Ma Wasu Mutane Yankan Rago A Jihar Neja
Next Post: Gwamnatin Gombe Ta Dauki Sabbin Matakan Tsaro

Karin Labarai Masu Alaka

Akwai Bukatar Bin Dokokin Tuki A Kan Hanyoyi Labarai
Kasar Zimbabwe Ta Samar Da Dokar Tsawaita Mulkin Mnangagwa Zuwa 2030 Labarai
Isra’ila Takai Sabon Hari Tehran Ranar Lahadi Labarai
Shugaban Najeriya Bola Tinubu Zai Ziyarci Jihohin Borno,Bauchi Da Legas Labarai
Yau Litinin Za’a Mika Daliban Ga Iyayen Su Labarai
Ana Cigaba Da Tattaunawa Tsakanin Trump Da Zelensky Domin Tsagaita Wuta A Ukraine Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • PDP Ta Tsayar da Goodluck Jonathan Takarar Shugaban Kasa
  • Hawan Gidan Gwamnati A Jihar Gombe
  • Hawan Babbar Sallah A Masarautar Kaltungo Dake Jihar Gombe
  • Sarkin Gombe Ya Yabi Nasarorin Inuwa Yahaya A Fannonin Tsaro Da Raya Kasa
  • Tinubu Ya Jaddada Aniyar Rage Tsadar Rayuwa Da Samar da Ayyukan Yi

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Nijar: Zamu Tsananta Bincike A Bakin Iyakokin Mu Afrika
  • Trump: Zamu Kawo Zaman Lafiya A Fadin Duniya Amurka
  • Gwamnatin Kano Ta Rufe Gidajen Bukukuwa Da Shakatawa Labarai
  • Jamhuriyar Nijar Ta Dakatar Da Bawa Amurkawa Visa Afrika
  • Man Da Matatar Dangote Take Fitarwa Zuwa Kasashen Afirka Ya Karu Afrika
  • Amurka Da Iran Sun Tattauna A Kasar Pakistan Afrika
  • Afrika Ta Kudu Ta Dora Haraji Mai Yawa Kan Karafa Afrika
  • An Samu Kaburbura Biyu Dauke Da Gawarwaki 173 A Kasar Kwango Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.