Kungiyar Darikar tijjaniya a Najeriya na ci gaba da nuna bukatar ganin gwamnatin Najeriya ta sako shehin Malami Sheik Sani Khalifa zariya da hukumomin kasar ke tsare dashi tun a watan disambar bara.
A Wani Babban taro da Kungiyar ta tijjaniya ta gudanar ta Bukaci Hukumomin Najeriyar da su hanzarta Sakin shehin Malamin.
Zargin alaka ta Kudi tsakanin shehin Malamin da wasu Sojojin da ake zargi da shirya juyin mulki yasa ake da Sheik Sani Khalifa zariya To Amma Kuma har ya zuwa wannan lokaci Hukumomin Najeriyar ba su bayyana hujjoji akan zargin ba.
Malam Ibrahim Aminu na daya daga cikin jagororin da Suka shirya Wannan taro Yace ya zuwa yanzu sun gano inda ake tsare da shehin Malamin Amma yace Gwamnatin Najeriya ta kullawa Malamin Sharri.
Ayanzu Kungiyar ta tijjaniya tace zata Fara Gudanar da Addu,o,I na Musamman domin neman hakkin malamin daga Allah Faruk Yusuf Balarabe da aka GI Sani da sidi sadauki shine Shugaban Matasan Tijjaniyar na Najeriya yace yanzu haka sun fara shirya yadda zasu Fara Gudanar da wadan Nan Addu,o,i…
Malam Muhammadu Kamilu Muridi ne na Sheik Khalifa zariya yayi Karin haske akan inda Suka sa gaba game da tsarin Addu,o,in.
yanzu a ranar goma ga wannan wata na Afirulu ne ake sa ran za,a ci gaba zaman koto domin sauraren wannan shari,a a Sheik Sani Khalifa zariya da Kuma Hukumomin Najeriyar.
Wakilin GTA Hausa Amurka Ke Magana Daga jihar Neja Mustapha Nasiru Batsari Yana dauke da cikekken rahoton


