Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojoji Sun Ceto Mutane 23, Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 19 A Cikin Sa’o’i 24 Afrika
  • 3G Taskforce Ya Dasa Bishiyoyi Don Kare Muhalli A Gombe Afrika
  • Builder Mahmood Yusuf Ya Tallafa Wa Mata Da Matasa Afrika
  • Gwamnan Jihar Bauchi Ya Jagoranci Tsohon Shugaban Kasar Najeriya Rangadi A Bauchi Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya Amince Da Naɗin Manyan Sakatarori 19 Afrika

Musa: “Da Yaddar Allah Zamu Ga Bayan Ta’addanci A Najeriya”
Published: December 5, 2025 at 5:18 AM | By: Yusuf Aliyu Harande

Jajircewa da muka nuna a baya ita ta sa Shugaba Bola Ahmad Tinubu, ya sake dauko ni don na ja ragamar ma’aikatar tsaro ta kasa. Tsarin aikin mu shine, ba nuna banbanci na addini ko kabilanci, haka kuma ba sani ba sabo wajen gabatar da aiki.

Mu duka ‘yan Najeriya ne sai mun hada hannu da tunanin mu waje daya sannan zamu iya samun zaman lafiya. Babban abun da yasa muke yin nasara shi ne son kasa da kishin ci gabanta.

Zamu hada kan dukannin jami’an tsaro waje daya, don ganin an yi aiki tare da samar da mafita ga kasa. A can baya mun fuskanci kalubale na rashin hadin kai, amma yanzu burin mu shine mu taho da kowa a cikin sabuwar tafiya.

Shugaban kasa ya dau alwashin bamu damar yin aiki ba tare da wata damuwa ba, ya kuma ce zai bamu dukkan wata gudunmawa da muke nema wajen kawo karshen ta’addanci a kasar. Na tabbatar ma sojoji wannan kudurin na aiki tukuru don kawo karshen matsalolin rashin tsaro a kasar.

Babban abun da muke nema shi ne gudunmawar Allah da ta jama’a wajen taya mu da addu’a da bada bayanan siri a duk lokacin da aka ga wani abu da bai yi tsari da zaman takewar al’ummah ba.

Duk wanda yake tare da Allah to zai ga nasara a cikin al’amuransa, don haka zamu yi aiki da kowa a wannan sabon matsayi.

Bamu da wani shiri na yin sulhu da ‘yan ta’adda, don kuwa basu da hujja ta kama talakawa da basu ji basu gani ba, mun dau damarar yakar su haikan, daga nan har illa-masha Allah.

Gwamnatin mu a shirye take taga mun kawo karshen ‘yan ta’adda a kowane hali, don haka muna neman addu’o’in ‘yan Najeriya a kowane hali da neman nasara akan duk bata gari.

https://gtahausa.com/wp-content/uploads/2025/12/1st-Report-Defence-Minister-Christopher-Musa-.mp3
Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Post navigation

Previous Post: Nnamdi Kanu Ya Nemi A Mayar Da Shi Abuja Daga Gidan Yarin Sokoto
Next Post: CAN: Da Alamu Daliban St. Mery Na Cikin Koshin Lafiya

Karin Labarai Masu Alaka

Jarman Deba Ya Kada Senata Goje A Zaben Fidda Gwani Afrika
Za A Cigaba Da Tattaunawa Domin Kawo Karshen Yakin Gabas Ta Tsakiya Amurka
Mali Da Burkina Faso Za Su Haramta Wa Amurkawa Izinin Shiga Ƙasashen Su Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Ahmed Gara Ya Kaddamar da Kofin Sarkin Gombe, Ya Jaddada Bunƙasa Matasa Afrika
Shugaban Amurka Zai Sake Aika Jirgin Yaki Gabas Ta Tsakiya Amurka
TIC Dutse Ta Nemi Ƙarin Tallafin Gwamnatin Jigawa Don Faɗaɗa Ayyukanta Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojoji Sun Ceto Mutane 23, Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 19 A Cikin Sa’o’i 24
  • 3G Taskforce Ya Dasa Bishiyoyi Don Kare Muhalli A Gombe
  • Builder Mahmood Yusuf Ya Tallafa Wa Mata Da Matasa
  • Trump Ya Yi Gargadi Kan Shirin Cire Shugaban FIFA Infantino
  • Katsina United Ta Yi Jimamin Mutuwar Ɗan Wasanta Ozoh

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Anakan Bincike Wajen Gano Dan Bindigar Da Ya Kashe Dalibai Biyu A Jihar Rhode Island Amurka
  • Man Da Matatar Dangote Take Fitarwa Zuwa Kasashen Afirka Ya Karu Afrika
  • Kungiyar ISIS Ta Dauki Alhakin Harin Kasar Nijar Afrika
  • Hukumar NAHCON Ta Bude Asibiti A Madina Afrika
  • Harin Makami Mai Linzami Da Rasha Ta Kai Yayi Barna Sosai A Ukraine Afrika
  • FRSC Gombe: Hatsarin Mota Ya Yayi Ajalin Mutane 38 Ya Jikkata Fiye Da 218 A Wata Ɗaya Najeriya
  • Trump Zai Sasanta Tsakanin Masar Da Habasha Amurka
  • China Da Jamhuriyar Dimokraɗiyya Kwango Sun Kulla Yarjejeniya Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.