An ƙaddamar da gasar Kofin Sarkin Gombe ta shekarar 2026 a ranar Asabar a filin wasan Pantami da ke jihar Gombe, tare da halartar sarakunan gargajiya, jami’an gwamnati, shugabannin wasanni da dubban masu sha’awar ƙwallon ƙafa.

Gasar, wadda ake gudanarwa duk shekara, tana haɗa masarautu da ƙananan hukumomin gargajiya daga sassan jihar domin ƙarfafa haɗin kai, zaman lafiya, fahimtar juna da kuma bai wa matasa damar nuna basirarsu ta fannin ƙwallon ƙafa.
Da yake jawabi a wajen bikin buɗe gasar, shugaban shirya gasar, Ahmed Shuaibu Gara Gombe, ya ce gasar ta zama wata muhimmiyar hanya ta gano da bunƙasa hazikan matasa a harkar wasanni tare da ƙarfafa zumunci tsakanin al’ummomin jihar.
Ya Bayyana cewa an bude Gasar da fafatawa Tsakanin Nafada da Gombe inda za’a Cigaba da bugawa a cibiyiyi uku da suka da da Cibiyar Bajoga, Deba da Billiri kuma Ya yabawa masarautu da suka yi rijista domin shiga gasar, yana mai bayyana cewa Masarautar Akko ce kaɗai ba ta shiga ba, tare da nuna fatan za ta shiga a bugu na gaba.
A nasa jawabin, Sarkin Gombe, Abubakar Shehu Abubakar III, wanda Madakin Gombe da Wakilin Birnin ya wakilta, ya jaddada goyon bayan masarautar ga gasar tare da yaba wa Ahmed Gara Gombe bisa ƙoƙarinsa na samar da damar bunƙasa matasa ta hanyar wasanni.

Shi ma shugaban Nigeria Football Federation, Ibrahim Musa Gusau, ya bayyana farin cikinsa kan yadda aka fara gasar, yana mai fatan za ta kasance mai cike da gasa cikin lumana da nuna bajinta.
Kamfanin GWG Sports Center Limited ne ya shirya tare da ɗaukar nauyin gasar ƙarƙashin jagorancin Ahmed Shuaibu Gara Gombe, a wani yunƙuri na ci gaba da tallafa wa ci gaban matasa da harkokin wasanni a jihar.

Masu bibiyar harkokin wasanni sun bayyana cewa Kofin Sarkin Gombe ya zama ɗaya daga cikin manyan gasa na matakin tushe a jihar, inda yake haɗa wasanni da al’adun gargajiya tare da ƙarfafa haɗin kan al’umma.
Ana sa ran wasannin za su ci gaba a makwanni masu zuwa yayin da ƙungiyoyi daga sassan Jihar Gombe ke fafatawa domin lashe kofin gasar ta shekarar 2026.


