Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Janar Rabe Abubakar Ya Mutu A Tsare A Hannun Masu Garkuwa Da Mutane Afrika
  • Anyi Jana’izar Dan Majalisar Wakilai Yaya Bauchi Tongo Afrika
  • Dan Majalisar Wakilai Yaya Bauchi Tongo Ya Rasu A Abuja Bayan Doguwar Jinya Afrika
  • Masu Luwadi Na Fuskantar Tara Da Daurin Shekaru 20 A Nijar Afrika
  • Sakon Shugaban Kasar Najeriya Bola Ahmed Tinubu A Ranar Dimokraɗiyya Ta 2026 Afrika

Ahmed Gara Ya Kaddamar da Kofin Sarkin Gombe, Ya Jaddada Bunƙasa Matasa
Published: June 13, 2026 at 8:47 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

An ƙaddamar da gasar Kofin Sarkin Gombe ta shekarar 2026 a ranar Asabar a filin wasan Pantami da ke jihar Gombe, tare da halartar sarakunan gargajiya, jami’an gwamnati, shugabannin wasanni da dubban masu sha’awar ƙwallon ƙafa.

Gasar, wadda ake gudanarwa duk shekara, tana haɗa masarautu da ƙananan hukumomin gargajiya daga sassan jihar domin ƙarfafa haɗin kai, zaman lafiya, fahimtar juna da kuma bai wa matasa damar nuna basirarsu ta fannin ƙwallon ƙafa.

Da yake jawabi a wajen bikin buɗe gasar, shugaban shirya gasar, Ahmed Shuaibu Gara Gombe, ya ce gasar ta zama wata muhimmiyar hanya ta gano da bunƙasa hazikan matasa a harkar wasanni tare da ƙarfafa zumunci tsakanin al’ummomin jihar.

Ya Bayyana cewa an bude Gasar da fafatawa Tsakanin Nafada da Gombe inda za’a Cigaba da bugawa a cibiyiyi uku da suka da da Cibiyar Bajoga, Deba da Billiri kuma Ya yabawa masarautu da suka yi rijista domin shiga gasar, yana mai bayyana cewa Masarautar Akko ce kaɗai ba ta shiga ba, tare da nuna fatan za ta shiga a bugu na gaba.

A nasa jawabin, Sarkin Gombe, Abubakar Shehu Abubakar III, wanda Madakin Gombe da Wakilin Birnin ya wakilta, ya jaddada goyon bayan masarautar ga gasar tare da yaba wa Ahmed Gara Gombe bisa ƙoƙarinsa na samar da damar bunƙasa matasa ta hanyar wasanni.

Shi ma shugaban Nigeria Football Federation, Ibrahim Musa Gusau, ya bayyana farin cikinsa kan yadda aka fara gasar, yana mai fatan za ta kasance mai cike da gasa cikin lumana da nuna bajinta.

Kamfanin GWG Sports Center Limited ne ya shirya tare da ɗaukar nauyin gasar ƙarƙashin jagorancin Ahmed Shuaibu Gara Gombe, a wani yunƙuri na ci gaba da tallafa wa ci gaban matasa da harkokin wasanni a jihar.

Masu bibiyar harkokin wasanni sun bayyana cewa Kofin Sarkin Gombe ya zama ɗaya daga cikin manyan gasa na matakin tushe a jihar, inda yake haɗa wasanni da al’adun gargajiya tare da ƙarfafa haɗin kan al’umma.

Ana sa ran wasannin za su ci gaba a makwanni masu zuwa yayin da ƙungiyoyi daga sassan Jihar Gombe ke fafatawa domin lashe kofin gasar ta shekarar 2026.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Nishadi, Sauran Duniya, Wasanni

Post navigation

Previous Post: Janar Rabe Abubakar Ya Mutu A Tsare A Hannun Masu Garkuwa Da Mutane

Karin Labarai Masu Alaka

Najeriya Ta Kai Wasan Kusa Da Na Karshe A Wasan Dambe Na Matasan Afirka Wasanni
Manchester United Ta Sallami Ruben Amorim Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Kasar Uganda Ta Tsare ‘Yan Jam’iyyun Adawa Dubu Biyu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Kasuwannin Hannun Jari Sun Farfado Afrika
Wani Jirgi Yayi Saukar Angulu Ba Shiri Najeriya
Birtaniya Zata Hana Jiragen Ruwan Rasha Wucewa Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Ahmed Gara Ya Kaddamar da Kofin Sarkin Gombe, Ya Jaddada Bunƙasa Matasa
  • Janar Rabe Abubakar Ya Mutu A Tsare A Hannun Masu Garkuwa Da Mutane
  • Anyi Jana’izar Dan Majalisar Wakilai Yaya Bauchi Tongo
  • Dan Majalisar Wakilai Yaya Bauchi Tongo Ya Rasu A Abuja Bayan Doguwar Jinya
  • Masu Luwadi Na Fuskantar Tara Da Daurin Shekaru 20 A Nijar

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Jihar Filato Ya Karbi Katin APC Labarai
  • Farashin Mai Ya Tashi A Kasuwannin Duniya Labarai
  • Shugaba Tinubu Ya Shiga Takara Wa’adi Na Biyu Afrika
  • Hukumomin Taliban Sunce A Shirye Suke Domin Sulhu Afrika
  • Shirin Dare 2030 UTC Yau Asabar 11.15.2025 Rediyo
  • Jihar Ekiti Ta Aiwatar Da Dokar Haraji Najeriya
  • Gwamnatin Tarayya Ta Bayyana Hadakar Ta Da Amurka Wajen Yakar ‘Yan Ta’adda Najeriya
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.