Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai Afrika
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari Afrika
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe Afrika
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS Afrika
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe Afrika

Shugaba Tinubu Ya Shiga Takara Wa’adi Na Biyu
Published: May 7, 2026 at 7:45 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Ranar Alhamis 7 ga watan Mayu ne, Mataimakin Shugaban Najeriya Kashim Shettima ya kaddamar da neman takarar Shugaba Bola Ahmed Tinubu a hukumance ga uwar jam’iyyar APC ta kasa.

A wani gagarumin taro da aka gudanar a dakin taro na *Bola Ahmed Tinubu International Conference Centre* Mataimakin ya jagoranci mambobin jam’iyyar da suka hada da gwamnoni, da yan majalisun tarayya, da sauran masu madafun iko na da da na yanzu, inda ya miƙa fom din neman takarar ga Shugabannin jam’iyyar a wani mataki na nuna goyon bayan masu madafun iko ga kudurin sake zaben shugaba Tinubu zango na biyu.

Da yake jawabi jim kadan bayan mika fom din, Mataimakin Shugaban Kasa Shettima ya bayyana shugaban a matsayin jagora mai juriya wanda ya yi nasarar Jan ragamar Najeriya zuwa tudun-mun tsira a yayinda guguwar matsalolin tattalin arziki ta so yin awon gaba da ita. Kashim ya kafa hujja da ajandar “Renewed Hope” a matsayin babban dalilin cancantar Shugaba Tinubu ga zagaye na biyu inda ya bayyana cewa sauye-sauyen da gwamnatin ta kawo sun fara samar da sakamako mai kyau, duk da tsaurin da suka zo da shi a karon farko.

“Kalubalen shekarun da suka gabata ba su raunana Shugaba Tinubu ba; maimakon haka ma sai kara masa kwarewa da suka yi,” in ji Shettima, inda ya ci gaba da cewa

“Wannan gwarzantaka da kwarewa da ya kara ne ya sa mu ke fatan kara masa wata dama”

A nata bangaren, uwar jam’iyyar ta kasa ta nuna cikakken goyon bayanta ga takarar, inda

Shugaban jam’iyyar APC na kasa, Farfesa Nentawe Yilwatda wanda ya karbi takardun takarar, ya ce ayyukan shugaba Tinubu a sassa daban-daban na farfado da kasar sun sa sake zaben nasa ya zama dole.

Yilwatda ya yi nuni da kyautatuwar tattalin arziki da karuwar kwarin gwiwar kasashen duniya ga makomar Najeriya a matsayin hujjojin da jam’iyyar ta dogara da su wajen amincewa da takarar Shugaba Bola Ahmed Tinubu.

Shi ma shugaban Majalisar Wakilai, Hon. Tajudeen Abbas ya yaba da garambawul din na shugaban Tinubu, wanda ya bayyana a matsayin harsashin farfadowar kasa mai dorewa.

Ita ma kungiyar Gwamnonin APC ta bakin Shugabanta kuma Gwamnan Jihar Imo, Hope Uzodinma wanda gwamnoni 12 suka rufa wa baya ta nuna goyon baya na bai-daya ga takarar

Gwamnonin da suka halarci taron su ne na jihohin Plateau, Ogun, Niger, Kaduna, Ondo, Katsina, Borno, Cross River, Taraba, Yobe, Nasarawa, da Bayelsa.

A yanzu dai mika tikitin takarar a hukumance ya kawo karshen rade-raden da ake yi game da aniyar shugaban ta neman wa’adin Mulki na biyu kamar yadda ta bayyana irin hadin kan Shugabanni na bai daya da ake dakon gani a zaben fitar da gwani na jam’iyyar APC.

Shugabannin jam’iyyar sun yi kira ga mambobinsu da su fito ƙwansu da ƙwarƙwatarsu don “kare fatan Najeriya.”.

Afrika, Labarai, Najeriya, Siyasa

Post navigation

Previous Post: Hukumar NAHCON Ta Bude Asibiti A Madina
Next Post: Ana Kokarin Kawo Karshen Matsalar Kashe Matafiya A Filato

Karin Labarai Masu Alaka

Mutum Mafi Tsufa A Saudiyya Ya Rasu Yana Da Shekaru 142 Labarai
Masu Ruwa da Tsaki akan Lamurran Siyasa sun Fara Maida Martani akan Matakin da Ministan Labaran Nigeria da wayar da kan Jama,a Idris Malagi na korar Daya Daga cikin Ma,aikatansa Saboda dalilai na Siyasa. da tsakiayar ranar Wannan larabace dai Mataimakin na Musamman akan yada Labarai ga Minista Malagi Malam Rani,u Ibrahim ya fitar da Wata sanarwar cewa Ministan ya Dakatar da Daya Daga cikin Ma,aikatansa Mai Suna Sa,idu Enagi Saboda ya fitar da Wani bayani a Kafar yada Labarai na sada zumunta dake Nuna Ministan ya shirya tsaf Domin takarar Gwamnan Jihar Neja a 2027. Malam Sa,idu Etsu Tsohon Dantakarar Shugaban cin Jam,iyyar APC a Nigeria Yace Matakin da Ministan ya Dauka yayi Dai dai Domin yanzu lokaci baiyi ba..ceu.. Shima Dattijon Siyasa a Jihar Neja Alh.Awaisu Giwa Kuta Yace Matakin da Ministan Labaran ya Dauka yayi Dai dai Domin yanzu Jihar Neja zaman Makoki Ake na fotinar Yan ta,adda ba wai Batun Neman Mukamin Siyasa ba..ceu .in.. To Sai jigon Jam,iyyar PDP Mai Adawa a Nigeria Hon.Yahaya Ability Yace Akwai kuskure Babba da Ministan ya tabka a dai dai Wannan Zamani na Siyasa duk da cewa Jihar Nejan na cikin Yanayi na masifar Yanbindiga..ceu..in .. Azaben Shekara ta 2023 Malagi ya kara yayi Takara Gwamnan Jihar Neja a jam,iyyar APC inda Gwamna Umar Bago ya kadashi a zaben fidda Gwani. Martanin Wasu ‘Yan Najeriya Ga Ministan Labarai Bisa Korar Dadiminsa Najeriya
Sama Da Zawiyya 100 Ne Suka Samu Tallafin Kayan Abinci Daga Al’mustapha Haji Sufi Labarai
Gwamnatin Bola Tinubu Ta Raba Taraktoci Dubu Biyu Domin Inganta Noma Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Sojin Kasar Congo Da ‘Yan Tawaye Sun Kara Shiga Yankin Uvira Labarai
Gwamnatin Najeriya Zata Farfado Da Cibiyar Koyon Sana’oi Ta Dangote Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Shugaban Amurka Donald Trump Ya Jadda da Kudirinsa Da Kwace Iyakar Greenland Amurka
  • Kungiyar HPV A Jihar Gombe Ta Jagoranci Yaki Da Karuwar Cutar Daji Afrika
  • Iran Zata Mayarwa Amurka Martanin Harin Kharg Afrika
  • ‘Yan Sandan Najeriya Sunyi Nasarar Hallaka ‘Yan Ta’adda A Katsina Afrika
  • Mutane Biyu Sun Mutu A Yayin Zaben Shugabannin Gundumomin APC A Jihar Ondo Najeriya
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Amurka Tana Ganawa Da Manyan Jami’an Leken Asiri Amurka
  • Shugaba Trump Ya Bukaci Kasar Iran Ta Mika Wuya Amurka
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.