Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

Gwamnan Jihar Kebbi Ya Amince Da Kasafin Kudi Mai Sauya Fasali Da Karfafa Rayuwar Al’umma
Published: December 16, 2025 at 5:44 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Gwamnan Jihar Kebbi, Kwamared Dokta Nasir Idris, Kauran Gwandu, ya rattaba hannu kan Dokar Kasafin Kuɗi ta shekarar 2026, wadda aka yi wa lakabi da “Kasafin Sauya Fasali da Ƙarfafa Al’umma”, lamarin da ya mayar da kasafin ya zama doka.

An gudanar da bikin sanya hannu a ranar Talata a Fadar Gwamnati da ke Birnin Kebbi, bayan Shugaban Majalisar Dokokin jihar Kebbi, Muhammad Usman Zuru, ya gabatar wa Gwamnan kasafin da Majalisar ta amince da shi.

Kasafin Kuɗin shekarar 2026 ya zo da jimillar kuɗi ₦642,930,818,157.99k, wanda ya haɗa da kuɗaɗen gudanarwa da na manyan ayyuka (recurrent da capital expenditures) domin shekarar kasafin kuɗi ta 2026.

Da yake jawabi, Shugaban Majalisar Dokokin Jihar, Alhaji Muhammad Usman Zuru, ya bayyana kasafin a matsayin wani muhimmin tarihi da aka cimma sakamakon kyakkyawar haɗin kai tsakanin ɓangaren zantaswa da na majalisa.

Zuru ya bayyana cewa Majalisar ta yi cikakken nazari, muhawara da tantance kasafin bisa tanade-tanaden kundin tsarin mulki da ƙa’idojin majalisa, kafin tura shi ga Gwamna domin amincewa.

Ya ƙara da cewa kasafin kuɗin 2026 ya bayyana hangen nesa na Gwamna Nasir Idris wajen samar da ci gaba mai ɗorewa, bunƙasa ababen more rayuwa, haɓaka ɗan Adam da walwalar al’ummar jihar Kebbi baki ɗaya.

Ya kuma jaddada cewa kyakkyawar fahimta tsakanin ɓangarorin biyu ta sanya jihar Kebbi ta zama abin koyi wajen kula da kuɗin gwamnati da shugabanci nagari.

Shugaban Majalisar ya kuma bayyana cewa cikin shekaru biyu kacal a wannan gwamnati, Majalisa ta 10 ta amince da dokoki 60, dukkaninsu kuma sun samu rattaba hannun Gwamna wani abin alfahari da ba a taɓa samun irinsa ba, wanda ke nuna girmamawar Gwamna ga dimokuraɗiyya da jajircewarsa wajen aiwatar da sauye-sauye.

Ya tabbatar da cikakken goyon bayan Majalisar ga manufofin ci gaban gwamnatin.

A nasa jawabin, Gwamna Nasir Idris ya nuna matuƙar godiya ga Shugaban Majalisar, da shugabannin majalisa da dukkan mambobinta bisa jajircewa, kishin ƙasa da mayar da hankali kan muradun al’umma wajen yin dokoki.

Gwamnan ya bayyana Majalisar a matsayin “Gidan Gaskiya na Al’umma”, yana mai cewa tsauraran matakan da Majalisar ke ɗauka wajen duba shawarwarin gwamnati na ƙara inganta shugabanci tare da tabbatar da cewa dokoki da manufofi sun dace da muradun al’ummar Jihar Kebbi.

Ya jaddada cewa gwamnatinsa ta yi aiki cikin cikakkiyar fahimta da Majalisa ba tare da rikici ba, yana mai cewa shugabanci haɗin kai ne, ba fafatawa ba, domin hidimar al’umma gaba ɗaya.

Gwamna Idris ya kuma nuna muhimmancin ƙara hanyoyin tara kuɗaɗen shiga na cikin gida (IGR), yana mai cewa nasarar aiwatar da kasafin 2026 na dogaro da inganta kudaden Shiga domin ƙara wa tallafin tarayya, wanda bai wadatar da bukatun ci gaban jihar ba.

Ya tabbatar da cewa kasafin ya fi ba da fifiko ga ayyukan da suka shafi al’umma kai tsaye, ƙarfafa matasa, bunƙasa ababen more rayuwa da inganta ayyukan gwamnati, tare da yin sassauci a inda ya dace domin samun fa’ida mafi girma ga jama’a.

A ƙarshe, Gwamnan ya jaddada jajircewar gwamnatinsa ga al’ummar Jihar Kebbi, tare da nuna kyakkyawan fata cewa haɗin kai tsakanin ɓangaren zangltaswa, majalisa da shari’a zai ƙara ƙarfi a 2026, wanda zai hanzarta ci gaba da samar da zaman lafiya mai ɗorewa.

Labarai, Najeriya

Post navigation

Previous Post: Domin Inganta Tsaro Najeriya Ta Sayi Jiragen Yaki A Kasar Italiya
Next Post: Ganduje: Mun Janye Shirin Kafa Hisbah Mai Zaman Kanta A Kano

Karin Labarai Masu Alaka

Rwanda Zata Janye Dakaru Daga Mozambique Afrika
Jihar Borno Ce Tayi Nasara A Gasan Karatun Al Qur’ani Na Kasa Najeriya
Aminu Tambuwal Ya Fice Daga PDP Ya Koma ADC Afrika
Amurka Ta Jefa Makamin Tomahawk A Makarantar Yara Mata Afrika
Amurka Zata Aika Jiragen Yaki Biyu Gabas Ta Tsakiya Amurka
Kasar Ghana Ta Bayyana Fataucin Bayi A Matsayin Babban Laifi Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Sakon Shugaban Kasar Najeriya Bola Ahmed Tinubu A Ranar Dimokraɗiyya Ta 2026 Afrika
  • Kabiru Vice: Najeriya Zata Iya Nasara A Kan Moroko AFCON 2025. Wasanni
  • Tinubu Ya Sayi Fom Din Takarar Shugaban Kasa Afrika
  • Dogarawan Ruwa Na Amurka Suna Yunkurin Shiga Wani jirgin Dakon Mai Da Aka Allakan Ta Da Venezuela Labarai
  • Shugaba Trump Da Gwamnan Minnesota Zasu Sassautawa Bakin Haure Amurka
  • Majalisa Ta Sanya Baki Akan Rikici Tsakanin Dangote Da Hukumar Albarkatun Mai Najeriya
  • Yakin Gabas Ta Tsakiya Ya Haifar Da Tsadar Taki Da Mai Ga Manoma Labarai
  • Amurka Na Gargadin Rwanda Da Ta Mutunta Alkawali Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.