Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai Afrika
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari Afrika
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe Afrika
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS Afrika
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe Afrika

Aminu Tambuwal Ya Fice Daga PDP Ya Koma ADC
Published: March 12, 2026 at 7:15 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Sanata Aminu Waziri Tambuwal, tsohon Gwamnan jihar Sokoto kuma Sanata mai wakiltar Mazabar Sokoto ta Kudu, ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar Peoples Democratic Party (PDP) tare da komawa jam’iyyar African Democratic Congress (ADC).

A cikin wata wasika mai kwanan wata 11 ga Maris, 2026 wadda ya aikewa da shugaban jam’iyyar PDP na gundumarsa ta Tambuwal/Shinfiri da ke Karamar Hukumar Tambuwal a jihar Sokoto, Sanata Tambuwal ya bayyana cewa ya ajiye zama dan jam’iyyar PDP nan take.

Tsohon Kakakin Majalisar Wakilai a Najeriyan ya bayyana cewa ya dauki wannan mataki ne bayan zurfin tunani da kuma tuntuba mai fadi da abokan siyasa da magoya bayansa.

A cewarsa, rikice-rikicen cikin gida, sabanin ra’ayi tsakanin shugabannin jam’iyyar da kuma rarrabuwar kawuna da ke ci gaba da addabar PDP sun sa ya zama da wahala a gare shi ya ci gaba da kasancewa a cikinta.

Ya kara da cewa wadannan matsaloli sun raunana hadin kai da kuma alkiblar da jam’iyyar ta tsaya a kai a baya.

Sanata Tambuwal ya kuma nuna godiyarsa ga jam’iyyar PDP bisa damar da ta ba shi ya yi wa kasa hidima a mukamai daban-daban, ciki har da Kakakin Majalisar Wakilai da kuma Gwamnan jihar Sokoto na wa’adi biyu.

Bayan sanar da ficewarsa daga PDP, Sanata Tambuwal ya tabbatar da cewa ya shiga jam’iyyar ADC tare da wasu daga cikin abokan siyasa da magoya bayansa.

Ya bayyana cewa matakin ya samo asali ne daga yakinin da yake da shi na cewa Najeriya na bukatar wata dandalin siyasa mai karfi da za ta ginu kan gaskiya, rikon amana, hada kai da kuma cikakken kudurin bunkasa kasa.

Sanatan ya sake jaddada aniyarsa ta ci gaba da yi wa Najeriya hidima tare da kare muradun dimokuradiyya, adalci da hadin kan kasa.

Afrika, Labarai, Najeriya, Siyasa

Post navigation

Previous Post: Kasar Gabon Ta Nemi Tallafin Asusun Bada Lamuni Na IMF
Next Post: Nan Gaba Kadan Kwallon Badminton Zata Samu Karbuwa Kamar Kwallon Kafa A Duniya

Karin Labarai Masu Alaka

Gwamnonin Arewa Maso Yammacin Najeriya Sun Halarci Taron Inganta Makashi A Birnin Landan Afrika
An Gano Gawar Dan Yawon Bude Ido A Kasar Chadi Afrika
Shugaban Kasar Ivory Coast Yayi Sauye-Sauye A Majalisar Ministocin Kasar Siyasa
An Gudanar Da Idin Karamar Sallah A Birnin Niamey Labarai
Wani Jirgin Sama Ya Karya Dokar Hana Zirga Zirga Amurka
Mayakan Houthi Zasu Shiga Yakin Amurka Da Isra’ila Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Za’a Dauko Messi Aro Zuwa Barcelona Deco Wasanni
  • Sojojin Da Suka Kifar Da Farar Hula A Guinea-Bissau Sun Sanar Da Cewa! Afrika
  • Kotu Ta Bada Belin Kwamishinan Kudin Jihar Bauchi Najeriya
  • Wata Kotu A Abuja Ta Wanke Abba Kyari Afrika
  • NAHCON Ta Kaddamar da Tawagar Malamai Afrika
  • ‘Yan Ta’adda Sun Hallaka Malaman Makaranta A Tilabery Afrika
  • Rahoton MDD Yace An Kashe Fiye Da Farar 1000 A Sudan Labarai
  • Shugaban Kasar Madagascar Ya Kori Prime Minista Da ‘Yan Majalisa Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.