Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro Labarai
  • Za A Cigaba Da Tattaunawa Domin Kawo Karshen Yakin Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Aminu Tambuwal Ya Fice Daga PDP Ya Koma ADC
Published: March 12, 2026 at 7:15 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Sanata Aminu Waziri Tambuwal, tsohon Gwamnan jihar Sokoto kuma Sanata mai wakiltar Mazabar Sokoto ta Kudu, ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar Peoples Democratic Party (PDP) tare da komawa jam’iyyar African Democratic Congress (ADC).

A cikin wata wasika mai kwanan wata 11 ga Maris, 2026 wadda ya aikewa da shugaban jam’iyyar PDP na gundumarsa ta Tambuwal/Shinfiri da ke Karamar Hukumar Tambuwal a jihar Sokoto, Sanata Tambuwal ya bayyana cewa ya ajiye zama dan jam’iyyar PDP nan take.

Tsohon Kakakin Majalisar Wakilai a Najeriyan ya bayyana cewa ya dauki wannan mataki ne bayan zurfin tunani da kuma tuntuba mai fadi da abokan siyasa da magoya bayansa.

A cewarsa, rikice-rikicen cikin gida, sabanin ra’ayi tsakanin shugabannin jam’iyyar da kuma rarrabuwar kawuna da ke ci gaba da addabar PDP sun sa ya zama da wahala a gare shi ya ci gaba da kasancewa a cikinta.

Ya kara da cewa wadannan matsaloli sun raunana hadin kai da kuma alkiblar da jam’iyyar ta tsaya a kai a baya.

Sanata Tambuwal ya kuma nuna godiyarsa ga jam’iyyar PDP bisa damar da ta ba shi ya yi wa kasa hidima a mukamai daban-daban, ciki har da Kakakin Majalisar Wakilai da kuma Gwamnan jihar Sokoto na wa’adi biyu.

Bayan sanar da ficewarsa daga PDP, Sanata Tambuwal ya tabbatar da cewa ya shiga jam’iyyar ADC tare da wasu daga cikin abokan siyasa da magoya bayansa.

Ya bayyana cewa matakin ya samo asali ne daga yakinin da yake da shi na cewa Najeriya na bukatar wata dandalin siyasa mai karfi da za ta ginu kan gaskiya, rikon amana, hada kai da kuma cikakken kudurin bunkasa kasa.

Sanatan ya sake jaddada aniyarsa ta ci gaba da yi wa Najeriya hidima tare da kare muradun dimokuradiyya, adalci da hadin kan kasa.

Afrika, Labarai, Najeriya, Siyasa

Post navigation

Previous Post: Kasar Gabon Ta Nemi Tallafin Asusun Bada Lamuni Na IMF
Next Post: Nan Gaba Kadan Kwallon Badminton Zata Samu Karbuwa Kamar Kwallon Kafa A Duniya

Karin Labarai Masu Alaka

Tawagar Shirya Gasar Kwallon Sarakuna A Gombe Ta Ziyarci Masarautun Jihar Labarai
Jami’an Tsaro: Babu Abun Tashin Hankali Kan Shawagin Jiragen Amurka Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Alaka Na Cigaba Da Kamari Tsakanin Rwanda Da Barundi Labarai
Gwamnatin Jamhuriyar Nijar Na Kokarin Inganta Harkokin Noman Kasar Afrika
Trump Yace Amurka Ta Kai Hare-Hare Masu Yawa Akan ‘Yan Ta’adda A Najeriya Amurka
Kasashen Da Dama Na Neman Hanyar Cigaba Da Dakon Makamashi Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Shugaba Trump Ya Yabawa Iran Bisa Bude Mashigar Hormuz
  • Shugaba Tinubu Yasa Hannu Kan Dokar Kasafin 2026
  • Shugaba Tinubu Yace Bazai Bawa ‘Yan Najeriya Kunya Ba
  • Jami’an Askarawa A Zamfara Sun Kama Na’urorin Fashewa Da Makudan Kuɗaɗe
  • Jami’yar ADC A Najeriya Ta Kori Nafiu Bala

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • ‘Yan Bindiga Sun Kama Akalla Mutane 13 A Wani Coci A Jihar Kogi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ruwa Kamar Da Bakin Kwarya Ya Haifar Da Mutuwar Mutane A Nairobi Afrika
  • Gwamnatin Kano: Zamu Kara Daukar Malamai Domin Inganta Ilimi Najeriya
  • Birtaniya Zata Fara Raba Rigakafin Allurar Cutar Sankara Kimiya
  • Jami’an Tsaron Pakistan Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Labarai
  • APC Ta Yi Babban Taron Amincewa Da Shugabannin Jam’iyyar Ba Hamayya Afrika
  • Iran Tabada Tabbacin Cigaba Da Rufe Mashigar Hormuz Afrika
  • An Kashe Mutane 25 Yayin Kai Wasu Hare Hare Jihar Adamawa Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.