Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • PDP Ta Tsayar da Goodluck Jonathan Takarar Shugaban Kasa Afrika
  • Hawan Gidan Gwamnati A Jihar Gombe Afrika
  • Hawan Babbar Sallah A Masarautar Kaltungo Dake Jihar Gombe Afrika
  • Sarkin Gombe Ya Yabi Nasarorin Inuwa Yahaya A Fannonin Tsaro Da Raya Kasa Afrika
  • Tinubu Ya Jaddada Aniyar Rage Tsadar Rayuwa Da Samar da Ayyukan Yi Afrika

Turkiyya Ta Zargi Alakar Isra’ila Da Somaliya
Published: February 18, 2026 at 5:10 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Shugaban kasar Turkiyya Racep Tayyib Erdogan ya ce a ranar Talata, yarda da Isara’ila ta yi da Somaliland a matsayin kasa mai cin gashin kan ta ba zai amfani ita kan ta Somaliland din ko kuma yankin da ta tsage daga ciki ba.

Tun a watan Disambar bara ma shugaban na Turkiyya yayi irin wannan martani inda ya ce shawarar da Isra’ila ta yanke na yarda da Somaliland, wadda ke a yankin arewacin Somalia, da ta yi ikirarin samun ‘yancin kai a matsayin kasa mai cin gashin kan ta a shekarar 1991, ya sabawa doka, ya kuma zargi Isra’ila da son kawo hargitsi a yankin na Afirka.

Turkiyya, wadda ke cikin kungiyar kasashen NATO tana kara tasirin ta a kasashen Afirka a shekarun kwana kwanan nan, inda ta ke horar da jami’an tsaron Somalia, tare da samar da taimakon kawo ci gaban kasa, a madadin bata damar amfani da hanya mai muhimmanci ta fitar da kayyayaki. Yayin da ita kuma kasar Somalia ta Yanke duk wata alaka dake tsakanin ta da kasashen Haddaddiyar Daular Laraba, inda ta zarge su da yin tasiri wajen yarda da Somaliland da Isra’ila ta yi a matsayin kasa mai ‘yancin kai.

Afrika, Labarai

Post navigation

Previous Post: Musulmai A Kasashen Duniya Da Dama Sunfara Azumin Ramadan
Next Post: ‘Yan Gudun Hijira A Kasar Libya Suna Fuskantar Cin Zarafi

Karin Labarai Masu Alaka

Kasar Colombia Tare Da Amurka Zasu Fitar Da Man Venezuela Labarai
Karamar Sallah: Hukumar Kashe Gobara A Gombe Ta Kuduri Aniyar Kare Al’umma Afrika
Rundunar Wanzar Da Zaman Lafiya Ta Shirya Taron Masu Ruwa Da Tsaki A Jihar Filato Afrika
Yaki Ta Sararin Samaniya Ya Cigaba Tsakanin Amurka, Isra’ila Da Iran Afrika
‘Yan Sanda A Gombe Sun Jaddada Shirin Yaƙi Da Munanan Dabi’u Afrika
Majami’ar Anglican Zasuyi Taron Zaben Sabon Shugaba Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • PDP Ta Tsayar da Goodluck Jonathan Takarar Shugaban Kasa
  • Hawan Gidan Gwamnati A Jihar Gombe
  • Hawan Babbar Sallah A Masarautar Kaltungo Dake Jihar Gombe
  • Sarkin Gombe Ya Yabi Nasarorin Inuwa Yahaya A Fannonin Tsaro Da Raya Kasa
  • Tinubu Ya Jaddada Aniyar Rage Tsadar Rayuwa Da Samar da Ayyukan Yi

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Jakadan Kasar Sin a Najeriya Ya Ziyarci Tinubu Najeriya
  • Jam’iyar SDP Tana Gudanar Da Babban Taro A Bauchi Afrika
  • Nnamdi Kanu Ya Nemi A Mayar Da Shi Abuja Daga Gidan Yarin Sokoto Labarai
  • Ukraine Tana Cigaba Da Tattaunawa Da Amurka Domin Kawo Karshen Yakin Kasar Amurka
  • Kasashen Yankin Gulf Sun Bukaci Amurka Takawo Karshen Iran Afrika
  • Shugaba Trump Ya Amince Da Tsawaita Cinikayya Tsakanin Amurka Da Kasashen Afirka Afrika
  • Kungiyar ECOWAS Ta Koka Game Da Yawan Juyin Mulki A Kasashen Afirka Afrika
  • Rundunar Wanzar Da Zaman Lafiya Ta Shirya Taron Masu Ruwa Da Tsaki A Jihar Filato Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.