Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama Afrika
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara Afrika
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe Afrika
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro Afrika
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa Afrika

Turkiyya Ta Zargi Alakar Isra’ila Da Somaliya
Published: February 18, 2026 at 5:10 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Shugaban kasar Turkiyya Racep Tayyib Erdogan ya ce a ranar Talata, yarda da Isara’ila ta yi da Somaliland a matsayin kasa mai cin gashin kan ta ba zai amfani ita kan ta Somaliland din ko kuma yankin da ta tsage daga ciki ba.

Tun a watan Disambar bara ma shugaban na Turkiyya yayi irin wannan martani inda ya ce shawarar da Isra’ila ta yanke na yarda da Somaliland, wadda ke a yankin arewacin Somalia, da ta yi ikirarin samun ‘yancin kai a matsayin kasa mai cin gashin kan ta a shekarar 1991, ya sabawa doka, ya kuma zargi Isra’ila da son kawo hargitsi a yankin na Afirka.

Turkiyya, wadda ke cikin kungiyar kasashen NATO tana kara tasirin ta a kasashen Afirka a shekarun kwana kwanan nan, inda ta ke horar da jami’an tsaron Somalia, tare da samar da taimakon kawo ci gaban kasa, a madadin bata damar amfani da hanya mai muhimmanci ta fitar da kayyayaki. Yayin da ita kuma kasar Somalia ta Yanke duk wata alaka dake tsakanin ta da kasashen Haddaddiyar Daular Laraba, inda ta zarge su da yin tasiri wajen yarda da Somaliland da Isra’ila ta yi a matsayin kasa mai ‘yancin kai.

Afrika, Labarai

Post navigation

Previous Post: Musulmai A Kasashen Duniya Da Dama Sunfara Azumin Ramadan
Next Post: ‘Yan Gudun Hijira A Kasar Libya Suna Fuskantar Cin Zarafi

Karin Labarai Masu Alaka

Zulum Ya Tallafa Wa Mambobin NYSC Da Naira Miliyan 8.2 A Borno Afrika
Jamhuriyar Nijar Ta Dakatar Da Bawa Amurkawa Visa Afrika
An Gudanar Da Jana’izar ’Yan Jaridan Da Suka Rasu A Jihar Gombe Labarai
Kirana Ga ‘Yan Siyasar Arewa, Su Jira Sai 2031- Akume Labarai
Kamfanin Jiragen Saman Ethiopia Zai Kafa Babban Filin Jirgi Afrika
Kasar Israela Zata Gina Sansani A Gaza Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Yawan wadanda suka mutu a mummunan harin yanbindiga a Jihar kwaran Najeriya yakai 170 Najeriya
  • ‘Yan Bindiga Sun Jikkata Mutane A Arewacin Kasar Benin Afrika
  • Kasar Congo Ta Dau Alwashin Bin Tsari Wajen Rarraba Ma’adanai Afrika
  • Shugabannin Sojojin Najeriya sun Kai Ziyarar Aiki Maiduguri  Afrika
  • Ruwan Sama Yayi Ajalin Mutane 70 A Nairobi Afrika
  • Sakataren Harkokin Wajen Amurka Yace Rahoton Kasashe Biyar Akan Rasha Yana Dauke Da Damuwa Amurka
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Gana Da Shugaban Makaman Nukiliya Afrika
  • Kasar China Ta Sauka Daga Ragamar Bada Bashi Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.