Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19 Afrika
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027 Afrika
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki Afrika
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko Afrika

Turkiyya Ta Zargi Alakar Isra’ila Da Somaliya
Published: February 18, 2026 at 5:10 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Shugaban kasar Turkiyya Racep Tayyib Erdogan ya ce a ranar Talata, yarda da Isara’ila ta yi da Somaliland a matsayin kasa mai cin gashin kan ta ba zai amfani ita kan ta Somaliland din ko kuma yankin da ta tsage daga ciki ba.

Tun a watan Disambar bara ma shugaban na Turkiyya yayi irin wannan martani inda ya ce shawarar da Isra’ila ta yanke na yarda da Somaliland, wadda ke a yankin arewacin Somalia, da ta yi ikirarin samun ‘yancin kai a matsayin kasa mai cin gashin kan ta a shekarar 1991, ya sabawa doka, ya kuma zargi Isra’ila da son kawo hargitsi a yankin na Afirka.

Turkiyya, wadda ke cikin kungiyar kasashen NATO tana kara tasirin ta a kasashen Afirka a shekarun kwana kwanan nan, inda ta ke horar da jami’an tsaron Somalia, tare da samar da taimakon kawo ci gaban kasa, a madadin bata damar amfani da hanya mai muhimmanci ta fitar da kayyayaki. Yayin da ita kuma kasar Somalia ta Yanke duk wata alaka dake tsakanin ta da kasashen Haddaddiyar Daular Laraba, inda ta zarge su da yin tasiri wajen yarda da Somaliland da Isra’ila ta yi a matsayin kasa mai ‘yancin kai.

Afrika, Labarai

Post navigation

Previous Post: Musulmai A Kasashen Duniya Da Dama Sunfara Azumin Ramadan
Next Post: ‘Yan Gudun Hijira A Kasar Libya Suna Fuskantar Cin Zarafi

Karin Labarai Masu Alaka

Masoya Kungiyar Kwallon Kafar Morocco Suna Cikin Farin Ciki Bisa Hukuncin Kotu Afrika
Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Aikin Wutan Lantarki A Jami’ar Bayero Afrika
‘Yan Bindiga Sun Kashe Fiye Da Mutane 15 A Kasar Australiya Labarai
Ruwa Kamar Da Bakin Kwarya Ya Haifar Da Mutuwar Mutane A Nairobi Afrika
Sabuwar Dama Ga Masu Zaɓe: INEC Ta Tsawaita CVR Zuwa Ƙarshen Yuli Afrika
Akwai Bukatar APC Tayi Gyare-Gyare Kafun Zabe Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Kasar Saudiya Zata Cika Azumi Talatin Kimiya
  • Hukumomin Tsaron Kenya Sunce ‘Yan Kasar Suna Fafata Yaki Da Dakarun Rasha A Ukraine Afrika
  • Hawan Durba A Fadar Sarkin Zazzau Afrika
  • Amurka Ta Kwace Jirgin Mai Mallakar Rasha Amurka
  • Ga Fili Ga Doki Najeriya
  • Gwamnatin Tarayya Tana Neman Kudi Domin Aiwatar Da Kasafin Kudin 2026 Najeriya
  • Iran Tayi Allah Wadai Da Kai Hari Cibiyar Pars Afrika
  • Hamma Saleh Ya Yi Fatali da Bai Wa Pantami Takarar Gwamna a PDP Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.