Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Gana Da Shugaban Makaman Nukiliya
Published: February 17, 2026 at 11:13 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Ranar Litinin ministan harkokin wajen Iran ya gana da shugaban hukumar kayyade makaman Nukiliya na MDD, gabanin zaman shawarwari tsakanin hukumomi dake Washington da kuma Tehran, da zimmar warware takaddamakan shirin Nukiliyar Iran, da alamun babu bangare da yake nuna sassauci, yayinda Amurka take barazanar daukar matakin Soja kan Farisa.

Amurka wacce tare da Isra’la suka kai hare hare na hadin guiwa kan Iran a cikin watan Yunin bara, ta tura wani babban jirgin ruwa mai dakon jiragen yaki na sama, wanda shine na biyu zuwa gabas ta tsakiya baya ga wasu jiragen ruwan yaki da tuni suke can, a yayinda ake zaman kallon hadarin-kaji tsakanin kasashen biyu.

Wani lamari da ya kara zaman dar dar shine ganin Iran ta fara rawar daji a mashigan ruwan Hormuz, wata muhimmiyar mashigar  ruwa na kasa da kasa mai muhimmancin gaske ga kasashen larabawa da suke yankin Gulf, wadanda suka nemi a bi hanyoyin difilomasiyya wajen warware takaddamar.

A farkon watan nan ne Amurka da Iran suka sake farfado da shawarwari tsakanin su da nufin warware rikici kan shirin Nukiliyar Iran, wadda Washington da kawayenta a turai suke zargin na kera makamai ne, yayinda Iran kuma ta dage shirin ta na farar hula ne.

Afrika, Amurka, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Dan Ra’ayin Mazan Jiya Leo Brent Zai Kyautata Alakar Afirka Ta Kudu Da Amurka
Next Post: Dottin Shara Ya Damu Jama’ar Havana Kasar Cuba

Karin Labarai Masu Alaka

An Kai Shugaban Kasar Venezuela Kotu Amurka
An Samu Bullar Cutar COVID 19 A Najeriya Afrika
Kimanin Ganga Miliyan 40 Na Danyen Albarkatun Mai Yayi Kwantai A Kasashen Afirka Ta Yamma Afrika
Yeriman Ingila Ya Gana Da Yeriman Saudiya Mai Jiran Gado Amurka
Ankara Gano Wani Abu Mai Kama Da Abun Fashewa A Jabo Jihar Sokoto Tsaro
Kungiyar Miyetti Allah Ta Bukaci Mambobinta Su Marawa Dr. Jamilu Isiyaku Gwamna Baya A Gombe Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Tabbas Atiku Abubakar Ya Karbi Katin Jam’iyyar ADC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ana Cigaba Da Kai Kayan Agaji Kasar Morocco Sakamakon Tsananin Hunturu Afrika
  • Haɗin Gwiwar GOSERC Da Savannah Zai Ƙarfafa Rarraba Wutar Lantarki A Faɗin Jihar Gombe Afrika
  • ‘Yan Sandan Bauchi Sun Kama Mutum Biyu Kan Zargin Fashi da Makami A Gadau Afrika
  • Dubban ‘Yan Gudun Hijira Sun Halaka Amurka
  • Gwamnatin Tarayya Ta Cimma Yarjejeniya Da Kungiyar Malaman Jami’oi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Babban Malamin Musulunci Sheikh Usman Kusfa Zaria Ya Rasu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Kanal Sani: Idan ‘Yan-Ta’adda Zasu Mutunta Sulhu To Gwamnati Ta Duba Hakan Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.