Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Jarman Deba Ya Kada Senata Goje A Zaben Fidda Gwani Afrika
  • Jami’an ‘Yan Sanda A Gombe Sun Kama Barayi Afrika
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai Afrika
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari Afrika
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe Afrika

Dan Ra’ayin Mazan Jiya Leo Brent Zai Kyautata Alakar Afirka Ta Kudu Da Amurka
Published: February 17, 2026 at 9:49 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Mutumin da shugaban Amurka Donald Trump ya nada jakadan kasar a Afirka ta kudu, dan gwagwarmaya mai ra’ayin mazan jiya Leo Brent Bozell na uku, wanda kuma marubuci ne ya sauka kasar, inda zaiyi aiki domin gyara dangantaka tsakanin kasashen biyu wanda yayi tsami.

Wani jami’i a ofishin jakadancin Amurka ya fadawa kamfanin dilancin labarai na Reuters cewa, Ambasda Bozell ya iso. Kuma ana sa ran zai gabatarwa shugaba Cyril Ramaphosa takardunsa gabannin ya fara aiki.

Dangantaka tsakanin hukumomi a Washington da Pretoria sunyi baya ainun bara, yayinda Trump yake sukar kasar cewa tana muzgunawa tsiraru farar fata, ya soki mu’amalar kasar da Rasha da kuma China, sannan ya aza mata haraji mai yawa kan kayayyaki daga kasar.

Afirka ta kudu bada ta da jakada a Washington tun cikin watan Yunin bara, bayanda shugaba Trump ya kori jakadan Afirka ta kudu Ibrahim Rasool, daga kasar.

A lokacin da ake tantance shi cikin watan Oktoban bara, Ambasada Bozell yace zai tunkari aikinsa tare da girmamawa ga al’umar Afirka ta kudu, kuma yana ganin akwai damar kulla dangantaka mai dorewa duk da cewa akwai sassan da suke da sabanin ra’ayi.

Afrika, Amurka

Post navigation

Previous Post: ‘Yan Tawaye A Burkina Faso Sun Kashe ‘Yan Kasar Ghana
Next Post: Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Gana Da Shugaban Makaman Nukiliya

Karin Labarai Masu Alaka

Kasashen Amurka Da China Sun Matsawa Ghana Domin Rage Kudaden Haraji Afrika
Tarkacen Makamai Masu Linzami Sun Lalata Gidaje Da Wuraren Kasuwancin Palasdinawa Afrika
Nijar: Zamu Tsananta Bincike A Bakin Iyakokin Mu Afrika
Hamas Ta Kwance Damara Afrika
Hukumar Upper Benue Zata Inganta Noma A Dadinkowa Afrika
Fiye Da Fararen Hula 1000 Yunwa Ta Kashe A Sudan Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jarman Deba Ya Kada Senata Goje A Zaben Fidda Gwani
  • Jami’an ‘Yan Sanda A Gombe Sun Kama Barayi
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Za A Rantsar Da Mainasara Kogo A Matsayin Shugaban Kundin Da’ar Ma’aikata Labarai
  • CNG Ta Farfado Da Jarin Masu Adaidaita Sahu A Kaduna Afrika
  • Amurka Ta Kai ‘Yan Cirani Kamaru Afrika
  • Kotu A Kasar Tunisiya Ta Daure Wani Babban Dan Kasuwa Da Wasu ‘Yan Majalisa Afrika
  • Prime Ministan Senegal Ya Bayyana Shirin Sauya Sheka Afrika
  • Harin Isra’ila A Gaza Da Jirgi Maras Matuki Ya Kashe Mutane Afrika
  • Ministan Yaɗa Labarai: Ceto Daliban Neja An Samu Natsuwa A Kasa Labarai
  • Kabiru Vice: Najeriya Zata Iya Nasara A Kan Moroko AFCON 2025. Wasanni
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.