Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Najeriya Da Maroko Sun Kulla Yarjejeniya Afrika
  • Pantami Ya Bayyana Dalilin Mayar Da Zaben Sa Abuja Afrika
  • Jam’iyar SDP Tana Gudanar Da Babban Taro A Bauchi Afrika
  • Rundunar Wanzar Da Zaman Lafiya Ta Shirya Taron Masu Ruwa Da Tsaki A Jihar Filato Afrika
  • Najeriya Da Amurka Sun Karfafa Alakar Tsaro Afrika

Kungiyar ‘Yan Jarida Ta Najeriya Ta Tabbatar Da Kyautata Rayuwar Mambobin ta
Published: December 6, 2025 at 5:46 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Kungiyar Ƴan Jarida ta Najeriya ta sake tabbatar da aniyyarta na kare haƙƙin ’yan jarida da inganta walwalar su, yayin da ta bayyana nasarorin da ta cimma tare da sabbin shirye shiryen da take kaddamarwa a taron shugabannin yankin Arewa maso Gabas da aka gudanar a Yola, Jihar Adamawa.

Shugaban ƙungiyar na ƙasa, Kwamared Alhassan Yahaya Abdullahi, ya bayyana wannan kuduri a taron da aka yi a cibiyar NUJ ta Yola, inda ya jaddada bukatar haɗin kai domin farfaɗo da ƙarfinsu na ƙungiya a wannan lokaci da ake yawan samun barazana, tsangwama da cin zarafi ga ’yan jarida a sassa daban daban na ƙasar.

Kwamared Alhassan Yahaya Abdullahi ya bayyana cewa shirin ƙungiyar na inganta walwalar membobin ta ya haɗa da ƙaddamar da inshorar rayuwa da inshorar lafiya ga dukkan ’yan jarida masu aiki, yana mai nuna damuwa da cewa a halin yanzu, ƙasa da kashi ɗaya cikin ɗari na ’yan jarida ne ke da inshora.

Yace tsarin inshorar lafiyar zai yi daidai da sabon tsarin ƙasa domin rage nauyin kuɗin magani da suke biya daga aljihun su.

Ya ƙara da cewa ƙungiyar na ƙoƙarin ganin an inganta albashin ’yan jarida ta hanyar rubutawa da mika kudirin dokar Media Enhancement Bill ga Majalisar Dokoki ta tarayya domin a duba shi tare da amincewa.

Shugaban ya yi kira ga Gwamnan jihar Adamawa da ya tallafa wa ƙungiyar ta hanyar samar da sabuwar Mota kirar bas da kuma sake fasalin sakatariyar NUJ ta jihar domin inganta ayyukan ’yan jarida da jin daɗin su.

Ya kuma bayyana cewa ƙungiyar ta samu nasarar sakin ɗan jarida, Mista Matthew Ojo, wanda aka tsare a Jamhuriyar Benin, ta hanyar haɗin kai da jakadancin kasa da jami’an Najeriya.

Wannan, a cewar sa, wani babban misali ne da ke nuna yadda NUJ ke tsaya wa ’yan jarida, ko da kuwa ba cikakken mamba ba ne.

Labarai

Post navigation

Previous Post: Gwannatin Jihar Kebbi Ta Arawa Maniyyata Kuɗin Aikin Hajji 2026,
Next Post: Jirgin Sojin Saman Najeriya Yayi Hatsari a Jihar Neja

Karin Labarai Masu Alaka

Gwamnatin Najeriya Na Shirin Yin Zamiya Don Biyan Bashi Labarai
Shugaba Tinubu Ya Gana Da Takwaransa Na Kasar Jamus Akan Sha’anin Tsaro Labarai
Jirgi Marar Matuki Yayi Ajalin A Kallah Mambobin M23 9 Tare Da Kashe Kakakin Rundunar Afrika
Kenya Ta Cimma Yarjejeniya Da Kasar Rasha Afrika
Kasar Botswana Na Samun Kudaden Shiga Da Lu’ulu’u Labarai
‘Yan Daba Sunkai Hari Kasuwar Waya A Kano Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Najeriya Da Maroko Sun Kulla Yarjejeniya
  • Pantami Ya Bayyana Dalilin Mayar Da Zaben Sa Abuja
  • Jam’iyar SDP Tana Gudanar Da Babban Taro A Bauchi
  • Rundunar Wanzar Da Zaman Lafiya Ta Shirya Taron Masu Ruwa Da Tsaki A Jihar Filato
  • Dakaru Sun Hallaka ’Yan Ta’adda Masu Yawa – DHQ

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Kasar Botswana Na Samun Kudaden Shiga Da Lu’ulu’u Labarai
  • An Dakatar Da Daniel Bisa Zargin Fyade Wasanni
  • An Gudanar Da Taron Matasan Kasashe 6, Don Kawo Karshen Ta’addanci Wasanni
  • Hari Da Jirgi Marar Matuki Ya Kashe Mutane Da Dama A Darfur Labarai
  • Najeriya Ta Kai Wasan Kusa Da Na Karshe A Wasan Dambe Na Matasan Afirka Wasanni
  • AFCON 2025, Jerin Abubuwan Da Aka Haramta Wa Magoya Baya Wasanni
  • Soyinka Ya soki Yawan Jami’an Tsaron Da Ake Bai Wa Seyi Tinubu Najeriya
  • Rundunar Operation Endurance Peace Ta Gano Wajen Kera Makamai A Jihar Filato Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.