Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

Limamin Da Ya Ceci Kiristoci Lokacin Rikicin Addini A Jihar Filato Ya Rasu
Published: January 16, 2026 at 12:16 PM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: January 16, 2026

Limamin addinin Islama daya ya sami shahara har ya sami lambobin yabo kan zaman lafiya a jahar Filato, Imam Abdullahi Abubakar ya rasu a Jos.

Marigayi Imam Abdullahi Abubakar ya shahara a duniya ne biyo bayan sadaukar da kai da yayi na bada kariya ga mabiya addinin Kirista fiye da dari uku, bayan ‘yan bindiga sun kai musu hari a kauyen Yalwan Gindin Akwati dake karamar hukumar Barkin Ladi a shekarun baya.

A ranar Alhamis goma sha biyar ga watan Janairun dubu biyu da ishirin ta shida, da misalin karfe tara na dare ne, Allah ya karbi ran Imam Abdullahi Abubakar bayan fama da rashin lafiya.

Malamin, wanda yayi limanci a karkara, musamman a yankin da a baya ake samun yawan tashin hankali, ya taimaka kwarai wajen wanzadda zaman lafiya da hadin kai tsakanin mabiya addinai da kabilu daban-daban, wanda ya kai ga har kasashen duniya irin su Amurka da Saudi Arebiya da kungiyoyi masu zaman kansu da gwamnatocin tarayya da na jahar Filato suka bashi lambobin yabo da adadinsu ya kai goma sha hudu.

A zantawarsa da wakiliyar GTA Hausa a Jos, Zainab Babaji, kafin rasuwarsa, Imam Abdullahi Abubakar ya bayyana cewa yana sauke hakkinsa na zama da kowa lafiya ne, kamar yadda Allah ya hori al’umma suyi, don haka ya sadaukar da ransa wajen ceton Kirista fiye da dari uku, a lokacin da ‘yan bindiga suka mamayesu.

Imam yace a dalilin ayyukan zaman lafiya da yayi, ya sami lambobin yabo, ya kuma je aikin Hajji banda ganawa da yayi da manyan shugabannin duniya ciki har da marigayi, shugaban Najeriya, Muhammadu Buhari da wassu gwamnoni.

Malam Abdullahi Umar Hassan, na’ibin limamin masallacin da Imam Abdullahi Abubakar ya jagoranta, ya bayyana mamacin a matsayin mai son hada kan jama’a ba tare da nuna bambanci ba.

Malam Hassan yayi fatar Allah ya zabo wanda zai cike gurbin da Imam ya bari na wanzadda zaman lafiya.

Haka ma kafafen sada zumunta a yau Jumma’a sun cika da hotunan Imam Abdullahi Abubakar, musammman daga wadanda suka yi hulda dashi a lokacin da yake raye, suna bayyana alhininsu kan rashin dattijon, da zayyana irin ayyukan alkhairi da yayi na samadda zaman lafiya.

Ga Rahoton Zainab Babaji Daga Jos

https://gtahausa.com/wp-content/uploads/2026/01/AUD-20260116-WA0025.mp3
Labarai

Post navigation

Previous Post: Dan Tsohon Mataimakin Shugaban Kasar Najeriya Atiku Abubakar Ya Shiga Jam’iyyar APC
Next Post: Ana Zargin Wani Dan Kasar Libya Da Fataucin Mutane

Karin Labarai Masu Alaka

Gombe Da UNFPA Sun Ƙarfafa Haɗin Gwiwa Don Yaƙi Da Cutar Fistula Da Tamowa Afrika
Akwai Bukatar Nazari Game Da Dangantakar Iran Da Kasashen Gulf Amurka
Gwamna Abba Kabir Ya Zabi Garo A Matsayin Mataimaki Afrika
Hukumar Hakar Ma’adanai A Kasar Zambiya Ta Dakatar Da Ayyukanta Kimiya
ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro Labarai
Hotunan Hawan Sallah A Masarautar Bauchi Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • An Tsaurara Tsaro Yayin Da Tehran Ke Shirin Karɓar Masu Jimamin Ayatollah Khamenei Afrika
  • ‘Yan Uwan Wadanda Aka Kashe Sunkai Kara Kotu Amurka
  • An Harbo Jirgin Yakin Amurka A Iran Amurka
  • Gwamnatin Bauchi: Ta Kaddamar Da Kwamitin Ma’adanai Labarai
  • Dubban Mutane Sunyi Zanga-Zanga A Kasar Australia Afrika
  • Amurka Ta Gabatarwa Sassan Dake Yakar Juna A Sudan da Shirin Tsagaita Wuta Afrika
  • Tinubu Ya Yi Allah Wadai Da Kashe-kashen Jos Da Kaduna Afrika
  • Gwamnan Jihar Kebbi Ya Amince Da Biyan Hakkokin Tsofin Ma’aikata 800 Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.