Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Limamin Da Ya Ceci Kiristoci Lokacin Rikicin Addini A Jihar Filato Ya Rasu
Published: January 16, 2026 at 12:16 PM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: January 16, 2026

Limamin addinin Islama daya ya sami shahara har ya sami lambobin yabo kan zaman lafiya a jahar Filato, Imam Abdullahi Abubakar ya rasu a Jos.

Marigayi Imam Abdullahi Abubakar ya shahara a duniya ne biyo bayan sadaukar da kai da yayi na bada kariya ga mabiya addinin Kirista fiye da dari uku, bayan ‘yan bindiga sun kai musu hari a kauyen Yalwan Gindin Akwati dake karamar hukumar Barkin Ladi a shekarun baya.

A ranar Alhamis goma sha biyar ga watan Janairun dubu biyu da ishirin ta shida, da misalin karfe tara na dare ne, Allah ya karbi ran Imam Abdullahi Abubakar bayan fama da rashin lafiya.

Malamin, wanda yayi limanci a karkara, musamman a yankin da a baya ake samun yawan tashin hankali, ya taimaka kwarai wajen wanzadda zaman lafiya da hadin kai tsakanin mabiya addinai da kabilu daban-daban, wanda ya kai ga har kasashen duniya irin su Amurka da Saudi Arebiya da kungiyoyi masu zaman kansu da gwamnatocin tarayya da na jahar Filato suka bashi lambobin yabo da adadinsu ya kai goma sha hudu.

A zantawarsa da wakiliyar GTA Hausa a Jos, Zainab Babaji, kafin rasuwarsa, Imam Abdullahi Abubakar ya bayyana cewa yana sauke hakkinsa na zama da kowa lafiya ne, kamar yadda Allah ya hori al’umma suyi, don haka ya sadaukar da ransa wajen ceton Kirista fiye da dari uku, a lokacin da ‘yan bindiga suka mamayesu.

Imam yace a dalilin ayyukan zaman lafiya da yayi, ya sami lambobin yabo, ya kuma je aikin Hajji banda ganawa da yayi da manyan shugabannin duniya ciki har da marigayi, shugaban Najeriya, Muhammadu Buhari da wassu gwamnoni.

Malam Abdullahi Umar Hassan, na’ibin limamin masallacin da Imam Abdullahi Abubakar ya jagoranta, ya bayyana mamacin a matsayin mai son hada kan jama’a ba tare da nuna bambanci ba.

Malam Hassan yayi fatar Allah ya zabo wanda zai cike gurbin da Imam ya bari na wanzadda zaman lafiya.

Haka ma kafafen sada zumunta a yau Jumma’a sun cika da hotunan Imam Abdullahi Abubakar, musammman daga wadanda suka yi hulda dashi a lokacin da yake raye, suna bayyana alhininsu kan rashin dattijon, da zayyana irin ayyukan alkhairi da yayi na samadda zaman lafiya.

Ga Rahoton Zainab Babaji Daga Jos

https://gtahausa.com/wp-content/uploads/2026/01/AUD-20260116-WA0025.mp3
Labarai

Post navigation

Previous Post: Dan Tsohon Mataimakin Shugaban Kasar Najeriya Atiku Abubakar Ya Shiga Jam’iyyar APC
Next Post: Ana Zargin Wani Dan Kasar Libya Da Fataucin Mutane

Karin Labarai Masu Alaka

Kungiyar Maharba Da ‘Yan Sintiri Sun Samu Kyautar Motoci Labarai
Kotu A Kasar Faransa Ta Daure Lumbala Shekaru 30 Bisa Laifin Cin Zarafi Labarai
Akwai Nasara A Tattaunawar Da Akeyi Tsakanin Iran Da Amurka Afrika
Gwamnonin Arewa Sunyi Allah Wadai Da Matsalar Tsaro A Shiyar Labarai
Hukumomin Tsaron Kenya Sunce ‘Yan Kasar Suna Fafata Yaki Da Dakarun Rasha A Ukraine Afrika
Najeriya Da Kasar Saudiya Sun Kulla Yarjejeniyar Tsaro Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Gwamnatin Najeriya Ta Ayyana Ranakun Hutun Sallar Azumi
  • Kungiyar Gwamnonin Arewacin Najeriya Tayi Kakkausar Lafazi Game Da Harin Maiduguri
  • Tinubu, Akpabio da Ministoci 9 Zasu Tafi Ƙasar Birtaniya
  • Tinubu Ya Aika Manyan Hafsoshin Tsaro Borno
  • Lauyoyi Sun Gurfanar Da Wani A Kotu Bisa Fasa Korin Kiyashi A Kenya

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • ‘Yan Tawaye A Burkina Faso Sun Kashe ‘Yan Kasar Ghana Afrika
  • An Bukaci Mabiya Addinin Kirista Da Suyi Koyi Da Rayuwar Yesu Najeriya
  • Kotu Ta Bada Belin Abubakar Malami Bisa Wasu Sharruda Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ana Cigaba Da Bincike Game Da Mutuwar Matar Da Likita Ya Manta Almakashi A Cikinta A Kano Najeriya
  • Hukumar NAHCON Ta Kamallah Shirye Shiryen Hajjin 2026 A Kasar Saudiya Labarai
  • Shugaba Tinubu Ya Gabatar da Kasafin Kuɗin 2026 Najeriya
  • Kasar Spain Zata Bada Diyya Ga Iyalen Wadanda Da Suka Rasu A Hatsarin Jirgin Kasa Labarai
  • Farashin Gangar Mai Yayi Gagarumar Fadi A Kasashen Duniya Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.