Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro Labarai
  • Za A Cigaba Da Tattaunawa Domin Kawo Karshen Yakin Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Amurka Ta Gabatarwa Sassan Dake Yakar Juna A Sudan da Shirin Tsagaita Wuta
Published: November 26, 2025 at 4:04 PM | By: Nafisa Ahmad

Wakilin Amurka, Massad Boulos, ya ce Amurka ta gabatarwa da sassan dake yakar juna a kasar Sudan wani shiri na kulla tsagaita wuta, amma kuma babu daya daga cikin bangarorin da ya bayyana amincewarsa da shirin ya zuwa yanzu.

Boulos yace duk da cewa babu wanda ya nuna rashin yarda da abubuwan dake kumshe a cikin shirin da Amurka ta gabatar, rundunar sojojin Sudan ta shimfida wasu ka’idojinta wadanda yace ba za a iya cimmawa ba.

Mai yakar rundunar sojoji a wannan fadan, Rundunar Dakarun wucin gadi ta RSF, ta ayyana tsagaita wuta na radin kanta jiya Litinin kamar yadda Amurka ta nema. Amma a yau Talatar nan, rundunar sojojin Sudan ta ce ta fatattaki wani harin da aka kai kan wani sansaninta dake Babanusa a Jihar Kordofan ta yamma, inda a nan yanzu bakin daga take a yakin na Sudan.

A makon da ya shige shugaba Donald Trump yace zai sa baki domin ganin an kawo karshen  wannan fadan daya barke a tsakanin rundunar soja da ta RSF a watan Afrilun 2023 a sanadin gwagwarmayar neman shugabanci tsakanin sassan biyu. Wannan rikici ya haddasa bala’in yunwa mai tsanani da kashe-kashen kabilanci da kuma raba miliyoyi da matsugunansu.

A halin da ake ciki, kungiyar agaji ta likitoci mai suna Medicine Sans Frontier, ko MSF a takaice, ta fada a yau Talata cewa ta janye ma’aikatanta daga wani asibitin dake Darfur, a bayan da aka harbe wani mai tura keken daukar marasa lafiya har lahira.

Kungiyar tayi kira ga dakarun rundunar RSF dake rike da wannan yanki da su tabbatar da tsaron lafiyar ma’aikatan asibitin dake yankin tsakiyar Darfur.

Afrika

Post navigation

Previous Post: Ukraine Ta Bayyana Goyon Bayanta Ga Tsarin Cimma Yarjejeniya
Next Post: Sojoji Sun Yi Juyin Mulki A Guinea Bissau

Karin Labarai Masu Alaka

Zabebben Shugaban Hungary Yace Zaidawo Da Tsarin Dimokraɗiyya Afrika
Libya Ta Kulla Yarjejeniya Da Kasashen Faransa Da Amurka Afrika
An Kai Hari Da Jirgi Mara Matuki A Kusa Da Matatar Mai Din Kasar Sundan Afrika
Hukumar ‘Yan Sanda Ta Dawo Da Dokar Zirga Zirgar Babura A Jihar Gombe Afrika
Sakataren Kungiyar NATO Yayi Magana Da Hukumomin Kasashe Afrika
Babu Alamar Tsagaita Wuta A Yaki Da Akeyi Tsakanin Isra’ila Da Amurka Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jami’yar ADC A Najeriya Ta Kori Nafiu Bala
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro
  • ‘Yan Sanda Sun Kama Mutane 33 Bisa Zargin Kai Hari A Jihar Kwara
  • Papa Roma Leo Yayi Gargadi Game Da Rushewar Dimokraɗiyya
  • Jiragen Ruwa Suna Biyayya Ga Dokar Hana Ketare Ruwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Tsananta Hukunci Ga Masu Fyade Kan Takaita Cin Zarafin Yara Labarai
  • Sakataren Tsaron Amurka Yace Yaki Tsakanin Amurka Da Iran Zai Dauki Sabon Salon Amurka
  • Sojin Kasar Congo Da ‘Yan Tawaye Sun Kara Shiga Yankin Uvira Labarai
  • Ankara Kai Wani Harin Bom Birnin Maiduguri Afrika
  • Ronaldo Da Messi Ka Iya Hadu A Gasar Cin Kofin Duniya: Ta Ya Ya ? Wasanni
  • Tsohuwar Ministan Albarkatun Mai Ta Bayyana A Kotu Najeriya
  • Shugaban Kasar Iran Yace Kasar Bata Da Kiyayya Tsakaninta Da Amurkawa Afrika
  • Ko Meye Gaskiyar Rade-Radin Zanga-Zanga A Jos Dake Jihar Filato Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.