Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama Afrika
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara Afrika
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe Afrika
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro Afrika
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa Afrika

Amurka Ta Gabatarwa Sassan Dake Yakar Juna A Sudan da Shirin Tsagaita Wuta
Published: November 26, 2025 at 4:04 PM | By: Nafisa Ahmad

Wakilin Amurka, Massad Boulos, ya ce Amurka ta gabatarwa da sassan dake yakar juna a kasar Sudan wani shiri na kulla tsagaita wuta, amma kuma babu daya daga cikin bangarorin da ya bayyana amincewarsa da shirin ya zuwa yanzu.

Boulos yace duk da cewa babu wanda ya nuna rashin yarda da abubuwan dake kumshe a cikin shirin da Amurka ta gabatar, rundunar sojojin Sudan ta shimfida wasu ka’idojinta wadanda yace ba za a iya cimmawa ba.

Mai yakar rundunar sojoji a wannan fadan, Rundunar Dakarun wucin gadi ta RSF, ta ayyana tsagaita wuta na radin kanta jiya Litinin kamar yadda Amurka ta nema. Amma a yau Talatar nan, rundunar sojojin Sudan ta ce ta fatattaki wani harin da aka kai kan wani sansaninta dake Babanusa a Jihar Kordofan ta yamma, inda a nan yanzu bakin daga take a yakin na Sudan.

A makon da ya shige shugaba Donald Trump yace zai sa baki domin ganin an kawo karshen  wannan fadan daya barke a tsakanin rundunar soja da ta RSF a watan Afrilun 2023 a sanadin gwagwarmayar neman shugabanci tsakanin sassan biyu. Wannan rikici ya haddasa bala’in yunwa mai tsanani da kashe-kashen kabilanci da kuma raba miliyoyi da matsugunansu.

A halin da ake ciki, kungiyar agaji ta likitoci mai suna Medicine Sans Frontier, ko MSF a takaice, ta fada a yau Talata cewa ta janye ma’aikatanta daga wani asibitin dake Darfur, a bayan da aka harbe wani mai tura keken daukar marasa lafiya har lahira.

Kungiyar tayi kira ga dakarun rundunar RSF dake rike da wannan yanki da su tabbatar da tsaron lafiyar ma’aikatan asibitin dake yankin tsakiyar Darfur.

Afrika

Post navigation

Previous Post: Ukraine Ta Bayyana Goyon Bayanta Ga Tsarin Cimma Yarjejeniya
Next Post: Sojoji Sun Yi Juyin Mulki A Guinea Bissau

Karin Labarai Masu Alaka

Koriya Ta Arewa Ya Goyi Bayan Iran Wajen Zaben Sabon Jagora Mojtaba Khameni Afrika
Iran Tayi Allah Wadai Da Kai Hari Cibiyar Pars Afrika
Ghana Tayi Watsi Da Yarjejeniya Akan Hakar Ma’adanai Afrika
Tinubu Na Kokarin Rage Tsadar Sufuri Ta Hanyar Shirin CNG Afrika
Muhimmin Sako Ga Alhazai Dake Kasar Saudiya Afrika
Fargaba Ta Karu Duk Da Tsagaita Wuta Tsakanin Iran Da Amurka Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Shugaban Kasar Najeriya Ya Gabatar Da Kudi Fiye Da Naira Triliyan 58 A Matsayin Kasafin 2026 Najeriya
  • An Tsinci Gawar Yarinya A Gombe Najeriya
  • Gwamnatin Jihar Gombe Ta Haramta Sana’ar Bola Jari Tsaro
  • Majalisar Dokokin Rivers Zata Tsige Fubara Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Shugaba Tinubu Ya Umarci Janye ‘Yan Sanda Masu Gadin Ministoci Tsaro
  • Nnamdi Kanu Ya Nemi A Mayar Da Shi Abuja Daga Gidan Yarin Sokoto Labarai
  • Cutar Zazzabin Lassa Tayi Ajalin Mutum 1 Yayinda Mutane 11 Suka Kamu A Jihar Gombe Najeriya
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.