Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Rundunar ‘Yan Sandan Gombe Ta Kuɓutar da Yaro Daga Hannun Masu Garkuwa Afrika
  • Tinubu Ya Buɗe Katafaren Kamfanin Sarrafa Lithium Domin Bunƙasa Tattalin Arziki Afrika
  • Sojoji Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 1,597, Sun Ceto Mutane 1,516 – DHQ Afrika
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u Afrika
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa Afrika

‘Yan Uwan Wadanda Aka Kashe Sunkai Kara Kotu
Published: January 28, 2026 at 11:46 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

‘Yan uwan wasu mutane 2 da aka kashe sakamakon harin da sojin Amurka suka kai wani jirgin ruwa da ake zaton na dauke da muggan kwayoyi, da ya taso daga Venezuela sun kai kara gaban kotu kan yiwa ‘yan uwan nasu kisan sakaci ranar Talata. Sun yi ikirarin cewa an kashe ‘yan uwan nasu ne ta hanyar da ta sabawa doka, ta yadda sojoji ke harin jiragen ruwan farar hula.

Lawyoyin masu rajin kare hakki, sun gabatar da karar ne a wata babban kotun kasa ta Amurka da ke birnin Boston. Karar da ta kasance ta farko da aka gabatar tun tun da Amurka ta kai hari har sau 36 kan jiragen ruwa a tekun Carribean da na Pacific, bisa umarnin gwamnatin Donald Trump, abinda yayi sanadiyyar rayuka 126 tun watan Satumbar bara.

‘Yan uwan Chad Joseph da Rishi Samaroo, mutane biyu ‘yan kasar Trinidad, na daga cikin mutane 6 da aka kashe a wani hari da aka kai ranar 14 ga Watan Oktoba. karar da aka gabatar ta ce mutanen biyu suna noma ne da kamun kifi a Venezuela, kuma suna hanyar su ta komawa gida ne a Las Cuevas da ke Trinidad yayin da aka kai musu harin.

Lauyan masu gabatar da kara Brett Max na ofishin masu rajin kare hakki na American Civil Liberties Union, ya ce wannan kisa ne da bashi da hujja daga gwamnatin dake cin zarafin ikon mulki ba tare da fuskantar hukunci ba, kuma wannan kara da aka gabatar na bukatar bin hakki da kuma kare dokokin shari’a.

Kungiyar lauyoyin rajin kare hakki sun gabatar da karar ne karkashin dokar Mutuwa a Teku mai Zurfi (wato Death on High Seas Act) a turance, dokar da ta bawa ‘yan uwan mamata damar kai kara don kisan sakaci ga ‘yan uwan su da ya auku a babban teku ko teku me zurfi, da kuma dokar kisa ga baki (Alien Tort Statute), ta shekarar 1789, wadda ta bawa bakin haure damar kai kara gaban kotunan Amurka, idan Amurkan ta saba dokar kasa da kasa.

Mahaifiyar Chad Joseph, Lenore Burnley, da kuma ‘yar uwar Rishi Samaroo, Sallycar Korasingh ne suka kai karar, kuma suna neman diyya ne kawai daga gwamnatin Amurka kan kisan ‘yan uwan nasu, ba wai kotu ta bada umurnin hana kara kai hare-haren nan gaba ba.

Amurka

Post navigation

Previous Post: Tsananin Sanyi Ya Kashe Mutane 38 A Amurka
Next Post: Kasar Israela Zata Gina Sansani A Gaza

Karin Labarai Masu Alaka

Kasashen Faransa Da Italiya Sun Nuna Rashin Amincewa Da Matakan Sojoji Amurka
Isra’ila Zata Kai Hari Cibiyar Makamashin Iran Afrika
Baitul Malin Amurka Zata Bawa Venezuela Da Cuba Damar Sayar Da Mai Amurka
Iran Tana Duba Yiwuwar Cimma Yarjejeniya Da Amurka Afrika
Shugaba Trump Ya Hana Kaiwa Cuba Man Fetur Daga Venezuela Amurka
Ma’aikatar Tsaron Amurka Zata Kara Samar Da Makamai Amurka

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Rundunar ‘Yan Sandan Gombe Ta Kuɓutar da Yaro Daga Hannun Masu Garkuwa
  • Tinubu Ya Buɗe Katafaren Kamfanin Sarrafa Lithium Domin Bunƙasa Tattalin Arziki
  • Sojoji Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 1,597, Sun Ceto Mutane 1,516 – DHQ
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Sakataren Kungiyar NATO Yayi Magana Da Hukumomin Kasashe Afrika
  • ‘Yan Sanda A Finland Sun Kwace Jirgin Ruwan Kasar Rasha Afrika
  • Kamfanonin Jiragen Sama Suna Fama Da Karin Farashin Mai Labarai
  • Rundunar ‘Yan Sanda Sun Ceto Wani Daga Hannun Masu Garkuwa Najeriya
  • Tinubu Ya Buɗe Katafaren Kamfanin Sarrafa Lithium Domin Bunƙasa Tattalin Arziki Afrika
  • Amurka Ta Kai Hari Kan ‘Yan ISISI A Jihar Sakkwato Bisa Rokon Gwamnatin Najeriya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Kano: Zamu Kara Daukar Malamai Domin Inganta Ilimi Najeriya
  • Gwamnatin Jihar Kano Zata Kashe Makudan Kudade Ga Jama’ar Kano! Najeriya
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.