Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojoji Sun Ceto Mutane 23, Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 19 A Cikin Sa’o’i 24 Afrika
  • 3G Taskforce Ya Dasa Bishiyoyi Don Kare Muhalli A Gombe Afrika
  • Builder Mahmood Yusuf Ya Tallafa Wa Mata Da Matasa Afrika
  • Gwamnan Jihar Bauchi Ya Jagoranci Tsohon Shugaban Kasar Najeriya Rangadi A Bauchi Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya Amince Da Naɗin Manyan Sakatarori 19 Afrika

Gwamnatin Jihar Kano Zata Kashe Makudan Kudade Ga Jama’ar Kano!
Published: November 20, 2025 at 5:13 PM | By: Yusuf Aliyu Harande

Masana da manazarta a fannin tattalin arziki a Najeriya sun fara fashin baki akan kasafin kudi da Gwamnatin jihar Kano ta shirya domin tunkarar shekarar kudi ta badi.

A jiya Laraba ne dai gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf, ya gabatar da kasafin a zauren majalisar dokokin, inda yace gwamnatin jihar ta shirya kashe kusan naira triliyon guda da rabi a shekarar kudi ta 2026 dake tafe.

Yace bangaren ilimin shine ya samu kaso mafi tsoka da kashi 30 cikin dari, yayin da aka kebewa fannin ayyukan raya kasa kashi 68 na gundari kasafin, inda gwamnati zata maida hankali akan kammala ayyaka da ake gudanarwa tare da kirkiro wasu sabbi.

Sai dai masanin tattalin arziki, Dr. Abdussalam Kani, yace alkaluman dake cikin kasafin sun ci karo da alkaluman da aka fitar a yayin taro na masu ruwa da tsaki, da kwararru kan tattalin arziki da Jami’an gwamnatin Kano da akayi a kwanakin baya, game da hasashen abin da gwamnatin ka iya samu na kudaden shiga a badi.

Yace yanzu kalubale ne akan majalisar dokokin ta Kano ta dai-daita alkaluman kasafin na kusan Naira tiriliyon guda da rabi, domin kuwa sun zarce alkaluman da ke cikin takardar M-TEF, wadda aka mikawa majalisar dokokin gabanin gwamnan ya gabatar da kasafin.

Dr Abdussalam Kani yace takardar M-TEF, mai dauke da hasashen da masana da Jami’an gwamnati game da kudaden shiga na gwamnati a shekara ta 2026 wadda bai wuce naira biliyan dari takwas ba, kuma doka tace tilas ne kasafin da gwamna ya shirya yayi dai-dai da hasashen masana cikin takardar M-TEF.

A nasa bangaren, comrade Salisu Gambo, gudana cikin ‘yan gwagwarmayar shugabanci na gari a Najeriya, yace kamata yayi ace banaren tsaro na biye da na ilimi wajen samun kaso mafi tsoka a cikin kasafi, a don haka akwai bukatar majalisar dokokin ta sake nazarin kason da aka kebewa al’amuran tsaro a jihar.

A nan gaba ne, ake sa ran majalisar dokokin zata kira taron jin ra’ayin jama’a, domin karbar kasidu da shawarwari daga kungiyoyi da dedekun mutane kan yadda suke ganin za’a inganta kasafin domin ya dace da muhimman bukatun al’umar jihar ta Kano su fiye da miliyan 20.

https://gtahausa.com/wp-content/uploads/2025/11/Kasafin-Kudin-Jihar-Kano-2026.mp3
Najeriya

Post navigation

Previous Post: Madrid, Arsenal Da Chelsea Sun Fara Zaurancen Dan-Wasa Kenan Yildiz
Next Post: Kotun Tarayya Ta Yankewa Nnamdi Kanu Daurin Rai-da-Rai

Karin Labarai Masu Alaka

Shugaban Ƙasar Koriya Ta Arewa Ya Halarci Gwajin Makami Mai Linzamin Kasar Labarai
Kungiyar Miyetti Allah Ta Bukaci Mambobinta Su Marawa Dr. Jamilu Isiyaku Gwamna Baya A Gombe Afrika
Jami’an Tsaro Sun Dakile Safarar Makamai Daga Jos Zuwa Jihar Neja Afrika
Shugabannin Kiristoci Sun Halarci Filin Idi A Kaduna Domin Nuna Haɗin Kai Afrika
Rundunar Operation Endurance Peace Ta Gano Wajen Kera Makamai A Jihar Filato Afrika
Bayan Ya Ziyarci Kwankwaso Gawuna Zai Karbi Katin ADC Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojoji Sun Ceto Mutane 23, Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 19 A Cikin Sa’o’i 24
  • 3G Taskforce Ya Dasa Bishiyoyi Don Kare Muhalli A Gombe
  • Builder Mahmood Yusuf Ya Tallafa Wa Mata Da Matasa
  • Trump Ya Yi Gargadi Kan Shirin Cire Shugaban FIFA Infantino
  • Katsina United Ta Yi Jimamin Mutuwar Ɗan Wasanta Ozoh

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Amurka Zata Bada Gudunwa Ga Masu Zanga-Zanga A Iran Sauran Duniya
  • Kasashen Da Dama Na Neman Hanyar Cigaba Da Dakon Makamashi Afrika
  • Babban Sakataren MDD Yayi Allah Wadai Da Matakin Soja A Gabas Ta Tsakiya Afrika
  • Fiye Da Mutane 108 Sun Rasa Rayukansu A Ambaliyar Kenya Afrika
  • Shugaba Tinubu: Naji Dadin Sako Daliban Neja Da Aka Sace Labarai
  • Kasar Spain Zata Bada Diyya Ga Iyalen Wadanda Da Suka Rasu A Hatsarin Jirgin Kasa Labarai
  • Shugaban Amurka Yace Sojojin Amurka Dana Iran Sunyi Taho Mugama Amurka
  • Isra’ila Ta Cire Sunayen Wasu Mutane Biyu Cikin Wadanda Take Fako Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.