Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • PDP Ta Tsayar da Goodluck Jonathan Takarar Shugaban Kasa Afrika
  • Hawan Gidan Gwamnati A Jihar Gombe Afrika
  • Hawan Babbar Sallah A Masarautar Kaltungo Dake Jihar Gombe Afrika
  • Sarkin Gombe Ya Yabi Nasarorin Inuwa Yahaya A Fannonin Tsaro Da Raya Kasa Afrika
  • Tinubu Ya Jaddada Aniyar Rage Tsadar Rayuwa Da Samar da Ayyukan Yi Afrika

Gwamnatin Jihar Kano Zata Kashe Makudan Kudade Ga Jama’ar Kano!
Published: November 20, 2025 at 5:13 PM | By: Yusuf Aliyu Harande

Masana da manazarta a fannin tattalin arziki a Najeriya sun fara fashin baki akan kasafin kudi da Gwamnatin jihar Kano ta shirya domin tunkarar shekarar kudi ta badi.

A jiya Laraba ne dai gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf, ya gabatar da kasafin a zauren majalisar dokokin, inda yace gwamnatin jihar ta shirya kashe kusan naira triliyon guda da rabi a shekarar kudi ta 2026 dake tafe.

Yace bangaren ilimin shine ya samu kaso mafi tsoka da kashi 30 cikin dari, yayin da aka kebewa fannin ayyukan raya kasa kashi 68 na gundari kasafin, inda gwamnati zata maida hankali akan kammala ayyaka da ake gudanarwa tare da kirkiro wasu sabbi.

Sai dai masanin tattalin arziki, Dr. Abdussalam Kani, yace alkaluman dake cikin kasafin sun ci karo da alkaluman da aka fitar a yayin taro na masu ruwa da tsaki, da kwararru kan tattalin arziki da Jami’an gwamnatin Kano da akayi a kwanakin baya, game da hasashen abin da gwamnatin ka iya samu na kudaden shiga a badi.

Yace yanzu kalubale ne akan majalisar dokokin ta Kano ta dai-daita alkaluman kasafin na kusan Naira tiriliyon guda da rabi, domin kuwa sun zarce alkaluman da ke cikin takardar M-TEF, wadda aka mikawa majalisar dokokin gabanin gwamnan ya gabatar da kasafin.

Dr Abdussalam Kani yace takardar M-TEF, mai dauke da hasashen da masana da Jami’an gwamnati game da kudaden shiga na gwamnati a shekara ta 2026 wadda bai wuce naira biliyan dari takwas ba, kuma doka tace tilas ne kasafin da gwamna ya shirya yayi dai-dai da hasashen masana cikin takardar M-TEF.

A nasa bangaren, comrade Salisu Gambo, gudana cikin ‘yan gwagwarmayar shugabanci na gari a Najeriya, yace kamata yayi ace banaren tsaro na biye da na ilimi wajen samun kaso mafi tsoka a cikin kasafi, a don haka akwai bukatar majalisar dokokin ta sake nazarin kason da aka kebewa al’amuran tsaro a jihar.

A nan gaba ne, ake sa ran majalisar dokokin zata kira taron jin ra’ayin jama’a, domin karbar kasidu da shawarwari daga kungiyoyi da dedekun mutane kan yadda suke ganin za’a inganta kasafin domin ya dace da muhimman bukatun al’umar jihar ta Kano su fiye da miliyan 20.

https://gtahausa.com/wp-content/uploads/2025/11/Kasafin-Kudin-Jihar-Kano-2026.mp3
Najeriya

Post navigation

Previous Post: Madrid, Arsenal Da Chelsea Sun Fara Zaurancen Dan-Wasa Kenan Yildiz
Next Post: Kotun Tarayya Ta Yankewa Nnamdi Kanu Daurin Rai-da-Rai

Karin Labarai Masu Alaka

Najeriya Da Amurka Sun Karfafa Alakar Tsaro Afrika
Shugaban Najeriya Bola Tinubu Zai Ziyarci Jihohin Borno,Bauchi Da Legas Labarai
NNPC Da Wasu Kamfanoni Sunyi Yarjejeniyar Iskar Gas Najeriya
Ana Cigaba Da Bincike Game Da Mutuwar Matar Da Likita Ya Manta Almakashi A Cikinta A Kano Najeriya
Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe Afrika
‘Yan Sanda Sun Kama Mutane 33 Bisa Zargin Kai Hari A Jihar Kwara Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • PDP Ta Tsayar da Goodluck Jonathan Takarar Shugaban Kasa
  • Hawan Gidan Gwamnati A Jihar Gombe
  • Hawan Babbar Sallah A Masarautar Kaltungo Dake Jihar Gombe
  • Sarkin Gombe Ya Yabi Nasarorin Inuwa Yahaya A Fannonin Tsaro Da Raya Kasa
  • Tinubu Ya Jaddada Aniyar Rage Tsadar Rayuwa Da Samar da Ayyukan Yi

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Shugaba Saied Yana Cigaba Da Samun Goyon Bayan Al’ummar Kasar Tunisiya Afrika
  • An Gano Wasu Boma Bomai Da Aka Binne A Jihar Neja Najeriya
  • Kasar Canada Ta Amince A Shigar Da Motoci Kirar Kasar China Kasar Amurka
  • Ministan Tsaron Najeriya Badaru Yayi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Sallah Sai Ranar Juma’a A Najeriya: Fadar Sarkin Musulmi Afrika
  • PDP Zata Karbi Mulki 2027 Inji Shugabannin Jam’iyar Siyasa
  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Sojoji A Jihar Kebbi Afrika
  • Layin Raba Wutan Lantarki Na Najeriya Ya Fashe Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.