Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19 Afrika
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027 Afrika
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki Afrika
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko Afrika

Gwamnatin Jihar Kano Zata Kashe Makudan Kudade Ga Jama’ar Kano!
Published: November 20, 2025 at 5:13 PM | By: Yusuf Aliyu Harande

Masana da manazarta a fannin tattalin arziki a Najeriya sun fara fashin baki akan kasafin kudi da Gwamnatin jihar Kano ta shirya domin tunkarar shekarar kudi ta badi.

A jiya Laraba ne dai gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf, ya gabatar da kasafin a zauren majalisar dokokin, inda yace gwamnatin jihar ta shirya kashe kusan naira triliyon guda da rabi a shekarar kudi ta 2026 dake tafe.

Yace bangaren ilimin shine ya samu kaso mafi tsoka da kashi 30 cikin dari, yayin da aka kebewa fannin ayyukan raya kasa kashi 68 na gundari kasafin, inda gwamnati zata maida hankali akan kammala ayyaka da ake gudanarwa tare da kirkiro wasu sabbi.

Sai dai masanin tattalin arziki, Dr. Abdussalam Kani, yace alkaluman dake cikin kasafin sun ci karo da alkaluman da aka fitar a yayin taro na masu ruwa da tsaki, da kwararru kan tattalin arziki da Jami’an gwamnatin Kano da akayi a kwanakin baya, game da hasashen abin da gwamnatin ka iya samu na kudaden shiga a badi.

Yace yanzu kalubale ne akan majalisar dokokin ta Kano ta dai-daita alkaluman kasafin na kusan Naira tiriliyon guda da rabi, domin kuwa sun zarce alkaluman da ke cikin takardar M-TEF, wadda aka mikawa majalisar dokokin gabanin gwamnan ya gabatar da kasafin.

Dr Abdussalam Kani yace takardar M-TEF, mai dauke da hasashen da masana da Jami’an gwamnati game da kudaden shiga na gwamnati a shekara ta 2026 wadda bai wuce naira biliyan dari takwas ba, kuma doka tace tilas ne kasafin da gwamna ya shirya yayi dai-dai da hasashen masana cikin takardar M-TEF.

A nasa bangaren, comrade Salisu Gambo, gudana cikin ‘yan gwagwarmayar shugabanci na gari a Najeriya, yace kamata yayi ace banaren tsaro na biye da na ilimi wajen samun kaso mafi tsoka a cikin kasafi, a don haka akwai bukatar majalisar dokokin ta sake nazarin kason da aka kebewa al’amuran tsaro a jihar.

A nan gaba ne, ake sa ran majalisar dokokin zata kira taron jin ra’ayin jama’a, domin karbar kasidu da shawarwari daga kungiyoyi da dedekun mutane kan yadda suke ganin za’a inganta kasafin domin ya dace da muhimman bukatun al’umar jihar ta Kano su fiye da miliyan 20.

https://gtahausa.com/wp-content/uploads/2025/11/Kasafin-Kudin-Jihar-Kano-2026.mp3
Najeriya

Post navigation

Previous Post: Madrid, Arsenal Da Chelsea Sun Fara Zaurancen Dan-Wasa Kenan Yildiz
Next Post: Kotun Tarayya Ta Yankewa Nnamdi Kanu Daurin Rai-da-Rai

Karin Labarai Masu Alaka

‘Yan Sandan Najeriya Sunyi Nasarar Hallaka ‘Yan Ta’adda A Katsina Afrika
Sojojin Najeriya Sun Kwato Mutane Daga Hannun Masu Garkuwa Najeriya
Jam’iyyar APC Ta Rantsar Da Sabbin Shugabanni a Jihar Neja Labarai
Ma’aikatan Tattara Kudin Haraji Sunyi Rikici Da Masu Babura A Bauchi Najeriya
Gwamna Ododo Ya Gargadi Sarakunan Gargajiya Najeriya
Ana Cigaba Da Jimamin Rasuwar Mataimakin Gwamnan Bayelsa Najeriya

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Rundunar Sojin Najeriya Ta Dakile Harin ‘Yan Ta’adda A Jihar Borno Labarai
  • Farashin Mai Ya Doshi Dala 100 Kowacce Ganga Afrika
  • Shugaban Najeriya Tinubu Ya Amince Na Tura Jakadu Labarai
  • Kasashe 5 Da Ke Fama Da Matsanancin Zazzabin Cizon Sauro Rediyo
  • Jagoran Addinin Kirista A Kaduna Ya Rabawa Fiye Da Musulmai Dubu Kayan Abincin Azumi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Tsohon Lauyan Amurka Jack Smith Ya Fadi Maganganu Game Da Donald Trump Amurka
  • Farashin Mai Ya Fadi Fiye Da Dala Daya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Amy Hunt Ta Zama Sabuwar Tauraruwar Wasannin Guje-guje Ta Birtaniya Wasanni
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.