Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama Afrika
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara Afrika
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe Afrika
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro Afrika
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa Afrika

Hukumar NDLEA Ta Kama Miyagun Kwayoyi A Edo
Published: April 6, 2026 at 1:58 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Jami’an Hukumar Yaki da Sha da Fataucin Miyagun Kwayoyi ta Ƙasa (NDLEA), sun kai samame a wata babbar ma’ajiyar miyagun kwayoyi a jihar Edo, inda suka kwace kilogram 1,378 na tabar wiwi da ake zargin an ɓoye, tare da kama wani da ake zargi da hannu a lamarin.

Kwamandan NDLEA a jihar Edo, Dr. Mitchell Ofoyeju, ne ya bayyana hakan a ranar Litinin a Benin, yana mai cewa an gudanar da samamen ne a garin Igbanke da ke karamar hukumar Orhionmwon, bayan samun sahihan bayanan sirri.

Ofoyeju ya ce samamen ya kai ga kwato buhun huna 125 na busasshen ganye da ake zargin nau’in tabar wiwi ce ta skunk.

A cewarsa, an kama wani mutum mai shekaru 37 mai suna Roland Owie dangane da wannan kamen.

Kwamandan ya bayyana wannan nasara a matsayin gagarumar ci gaba a kokarin hukumar na dakile hanyoyin samar da miyagun kwayoyi da yaɗa su.

Afrika, Najeriya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Shugaba Bola Tinubu Ya Amince Da Inganta Wutan Lantarki A Kasar
Next Post: Iran Zata Kawo Karshen Yaki Da Isra’ila Da Amurka

Karin Labarai Masu Alaka

Kasar Mauritius Zata Rage Amfani Da Makamashi Afrika
Isra’ila Tace Bazata Sake Kai Hari Kan Cibiyar Gas Ta Iran Ba Afrika
Iran Ta Kai Hari Matatar Mai A Kuwait Afrika
Ana Cigaba Da Bincike Game Da Mutuwar Matar Da Likita Ya Manta Almakashi A Cikinta A Kano Najeriya
Shugaban Amurka Ya Ya Bukaci Iran Ta Mika Wuya Afrika
Rundunar Sojin Najeriya Ta Kubutar Da Wasu Mutane 31 Da Aka Yi Garkuwa Dasu Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Majalisar Tattalin Arzikin Najeriya Ta Bawa Gwamnan Kebbi Mukamin Kyautata Harkar Kiwo Najeriya
  • Ukraine Ta Mika Wa Amurka Daftarin Yarjejeniya Da Rasha Sauran Duniya
  • Gwamnatin Tarayya Tayi Baje Kolin Nasarorin Tinubu Afrika
  • An Gudanar Da Idin Karamar Sallah A Birnin Niamey Labarai
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Kotu Ta Bada Belin Kwamishinan Kudin Jihar Bauchi Najeriya
  • An Fara Azumin Watan Ramadan A Najeriya Da Sassan Duniya  Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Burkina Faso Ta Sako ‘Yan Najeriya 11 Najeriya
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.