Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Tsohuwar Jarumar Kannywood Wasila Ismail Ta Rasu Afrika
  • Za’a Fassara Hudubar Arfa Da Harshen Hausa Afrika
  • An Kamallah Jigilar Alhazain Najeriya Domin Hajjin 2026 Afrika
  • Bola Ahmed Tinubu Ya Lashe Zaben Fidda Gwani Na Shugaban Kasa A Gombe Afrika
  • APC Ta Ayana Tsohon Gwamnan Bauchi M.A Abubakar A Matsayin Dan Takarar Gwamna Afrika

Hukumar NDLEA Ta Kama Miyagun Kwayoyi A Edo
Published: April 6, 2026 at 1:58 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Jami’an Hukumar Yaki da Sha da Fataucin Miyagun Kwayoyi ta Ƙasa (NDLEA), sun kai samame a wata babbar ma’ajiyar miyagun kwayoyi a jihar Edo, inda suka kwace kilogram 1,378 na tabar wiwi da ake zargin an ɓoye, tare da kama wani da ake zargi da hannu a lamarin.

Kwamandan NDLEA a jihar Edo, Dr. Mitchell Ofoyeju, ne ya bayyana hakan a ranar Litinin a Benin, yana mai cewa an gudanar da samamen ne a garin Igbanke da ke karamar hukumar Orhionmwon, bayan samun sahihan bayanan sirri.

Ofoyeju ya ce samamen ya kai ga kwato buhun huna 125 na busasshen ganye da ake zargin nau’in tabar wiwi ce ta skunk.

A cewarsa, an kama wani mutum mai shekaru 37 mai suna Roland Owie dangane da wannan kamen.

Kwamandan ya bayyana wannan nasara a matsayin gagarumar ci gaba a kokarin hukumar na dakile hanyoyin samar da miyagun kwayoyi da yaɗa su.

Afrika, Najeriya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Shugaba Bola Tinubu Ya Amince Da Inganta Wutan Lantarki A Kasar
Next Post: Iran Zata Kawo Karshen Yaki Da Isra’ila Da Amurka

Karin Labarai Masu Alaka

Wani Bincike Ya Nuna Cewar Da Wuya Iran Ta Bude Mashigin Hormuz Afrika
Hawan Durba A Fadar Sarkin Zazzau Afrika
Jamhuriyar Dimokraɗiyya Kwango Zata Karbi ‘Yan Gudun Hijirar Da Amurka Ta kora Afrika
Jirgin Sama Mai Saukar Ungulu Ya Kashe Mutane Biyar A Tanzaniya Afrika
Kasashen Faransa Da Italiya Sun Nuna Rashin Amincewa Da Matakan Sojoji Amurka
‘Yan Daba Sunkai Hari Kasuwar Waya A Kano Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Tsohuwar Jarumar Kannywood Wasila Ismail Ta Rasu
  • Za’a Fassara Hudubar Arfa Da Harshen Hausa
  • An Kamallah Jigilar Alhazain Najeriya Domin Hajjin 2026
  • Bola Ahmed Tinubu Ya Lashe Zaben Fidda Gwani Na Shugaban Kasa A Gombe
  • APC Ta Ayana Tsohon Gwamnan Bauchi M.A Abubakar A Matsayin Dan Takarar Gwamna

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Anyi Taho Mugama Tsakanin ‘Yan Sandan Turkiyya Da ‘Yan Kungiyar ISIS Afrika
  • Motar Yashi Ta Kashe Mutane Shida A Wani Coci Dake Legas Najeriya
  • Kungiyar ECOWAS Ta Koka Game Da Yawan Juyin Mulki A Kasashen Afirka Afrika
  • Mutane Da Yawa Ke Mutuwa A Dalilin Shan Magani Ba Bisa Ka’ida Ba Kiwon Lafiya
  • Hawan Sallah A Jihar Katsina Afrika
  • Akwai Shakku Akan Sanin Wacce Kungiyar Kwallon Kaface Zata Lashe Gasar Kofin Afirka Da Akeyi A Morocco Nishadi
  • Kotu Ta Bada Belin Abubakar Malami Bisa Wasu Sharruda Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Sojoji Sun Dakile Harin ’Yan Ta’adda a Kukareta Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.