Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Jihar Adamawa Fintiri Ya Koma APC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa
Published: February 28, 2026 at 2:17 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Gwamnatin Tarayyar Najeriya ta bukaci daukacin ‘yan Najeriya dake zaune a kasar Iran da sauran kasashen yankin tekun fasha (Gulf) da su kasance cikin tsananin sa ido da kiyaye kai, biyo bayan takun-saka da hare-haren soji da suka barke a yankin.

A wata sanarwa da Ma’aikatar Harkokin Waje ta fitar a ranar Asabar, 28 ga Fabrairu, 2026, wadda kakakin ma’aikatar, Kimiebi Imomotimi Ebienfa ya sanya wa hannu, gwamnatin ta bayyana cewa tana sanya idanu sosai kan yadda al’amura ke sauyawa bayan hare-haren da Isra’ila da Amurka suka kai kan wasu wurare a Iran, da kuma martanin da ita ma Iran din ta mayar.

Don tabbatar da tsira da lafiyar ‘yan kasa, ma’aikatar ta fitar da wasu shawarwari guda biyar (5) kamar haka:-
* Gwamnati ta shawarci ‘yan Najeriya da su guji zirga-zirga a kusa da sansanonin soji, gine-ginen gwamnati, ko wuraren da ake ganin za su iya zama matattarar rikici.

* An bukaci mutane da su zauna a gida muddin ba wata muhimmiyar bukata ce ta fitar da su ba, sannan su guji shiga taron jama’a ko zanga-zanga.

* An bukaci ‘yan kasa da su kiyaye dukkan dokoki da matakan tsaro da hukumomin kasashen da suke ciki suka gindaya.

* Ma’aikatar ta bukaci mutane da su rinka sauraron kafafen yada labarai na kasa da kasa masu gaskiya, sannan su kiyayi yada labaran bogi.

* Sanarwar ta tabbatar da cewa ofisoshin jakadancin Najeriya da ke Tehran (Iran), Qatar, Bahrain, Kuwait, Hadaddiyar Daular Larabawa (UAE), da Saudi Arabiya suna cikin shirin ko-ta-kwana don tallafa wa duk wani dan Najeriya da ya shiga cikin matsala.

A karshe, Gwamnatin Najeriya ta yi kira ga daukacin bangarorin da rikicin ya shafa da su kwantar da hankalinsu, su ajiye makamai su koma kan teburin tattaunawa domin samar da zaman lafiya a duniya.

Ta kuma sake jaddada cewa kare rayukan ‘yan Najeriya a duk inda suke a fadin duniya shi ne babban burin gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu.

Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya

Post navigation

Previous Post: Iran Ta Rufe Sararin Samaniyar Ta
Next Post: Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran

Karin Labarai Masu Alaka

Soyinka Ya soki Yawan Jami’an Tsaron Da Ake Bai Wa Seyi Tinubu Najeriya
Wata Tankar Mai Ta Kife A Apapa Legas Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Shugaban Najeriya Bola Tinubu Zai Ziyarci Jihohin Borno,Bauchi Da Legas Labarai
Kungiyar Kwadago Ta Shirya Zanga-Zanga A Najeriya Najeriya
Majalisar Tattalin Arzikin Najeriya Ta Bawa Gwamnan Kebbi Mukamin Kyautata Harkar Kiwo Najeriya
‘Yan Jarida Sunyi Mummunan Hatsari A Bauchi Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Kungiyar Gwamnonin Arewacin Najeriya Tayi Kakkausar Lafazi Game Da Harin Maiduguri
  • Tinubu, Akpabio da Ministoci 9 Zasu Tafi Ƙasar Birtaniya
  • Tinubu Ya Aika Manyan Hafsoshin Tsaro Borno
  • Lauyoyi Sun Gurfanar Da Wani A Kotu Bisa Fasa Korin Kiyashi A Kenya
  • Anfara Gangamin Kafa Dokoki Masu Tsanani Ga ‘Yan Luwadi A Senegal

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Shugaban Hukumar Hana Yaduwar Cututtuka A Afirka Yace Akwai Rashin Fahimta A Tsakanin Kasashen Da Amurka Take Tallafawa Afrika
  • Amurka Ta Gabatarwa Sassan Dake Yakar Juna A Sudan da Shirin Tsagaita Wuta Afrika
  • ‘Yan Bindiga Sun Hallaka Mutane A Kauyuka Dake Yammacin A Najeriya Najeriya
  • Gwamna Abba Gida-Gida Na Dari-Darin Shiga APC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Dusar Kankara Ta Hana Jirage Tashi A Birnin Paris Labarai
  • An Dakatar Da Daniel Bisa Zargin Fyade Wasanni
  • Sojojin Najeriya Sun Kashe Fitaccen ’Yan Bindiga Kallamu A Jihar Sakkwato Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Shugaba Trump Ya Bukaci A Cigaba Da Zanga Zanga A Iran Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.