Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • APC: Tinubu Da Shettima Za Su Sake Neman Wa’adi Na Biyu A 2027 Afrika
  • Sabuwar Sakatariyar Ƙungiyar Gwamnonin Arewa Za Ta Ƙarfafa Ayyukan Ci Gaban Yankin Afrika
  • TIC Dutse Ta Nemi Ƙarin Tallafin Gwamnatin Jigawa Don Faɗaɗa Ayyukanta Afrika
  • Gobara Ta Lalata Babban Zauren Majami’ar ECWA Gospel A Gombe Afrika
  • Gombe: ‘Yan Sanda Sun Tarwatsa Ƙungiyar Masu Fashi Da Damfara Ta Yanar Gizo Afrika

Rundunar ‘Yan Sandan Kebbi Ta Dakile Yunkurin Garkuwa Da Mutune, Ta Kama Masu Laifi
Published: July 6, 2026 at 6:35 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Kebbi ta kama wasu mutane huɗu da ake zargi da haɗa baki wajen aikata laifi, yin barazanar garkuwa da mutum ta hanyar kira da saƙonnin waya ba tare da bayyana ainihin su ba, tare da neman kuɗin fansa har Naira miliyan 30.

Mai magana da yawun rundunar, SP Bashir Usman, ya bayyana cewa an kama waɗanda ake zargin ne bayan wani mazaunin garin Jega, Alhaji Aminu Garba, ya kai rahoton cewa yana karɓar kiraye-kirayen waya masu ɗauke da barazanar yin garkuwa da shi idan har bai biya Naira miliyan 30 ba.

Waɗanda aka kama sun haɗa da Muhammad Shafiu mai shekaru 21, Mansur Ibrahim mai shekaru 21, Aliyu Umar mai shekaru 25 da kuma Muhammad Suleiman mai shekaru 23.

Binciken farko ya nuna cewa mutane uku daga cikin waɗanda ake zargin sun sayi sabon layin waya, sannan suka riƙa kiran wanda abin ya shafa, inda ɗaya daga cikinsu ya canja murya domin ta yi kama da ta Bafullatani, da nufin tsoratar da wanda ake yi wa barazanar tare da ɓoye ainihin sa.

Binciken ya kuma gano cewa Muhammad Suleiman, wanda ake zargin abokin iyalan wanda aka yi wa barazanar ne, ya bayar da lambar wayarsa da wasu bayanan iyalansa, waɗanda aka yi amfani da su wajen aiwatar da wannan shiri.

Rundunar ta ce jami’anta sun samu nasarar gano tare da cafke waɗanda ake zargin a ƙauyukan Gumbin Kure da Gamjeji da ke Ƙaramar Hukumar Maiyama, lamarin da ya dakile shirin kafin a aiwatar da shi.

Kwamishinan ‘Yan Sandan Jihar Kebbi, CP Umar M. Hadejia, ya ba da umarnin zurfafa bincike tare da gurfanar da waɗanda ake zargin a gaban kotu bisa tanadin doka.

Ya kuma jaddada kudirin rundunar na kare rayuka da dukiyoyin al’umma, yana mai gargadin cewa duk wanda aka samu da hannu a laifukan garkuwa da mutane, karɓar kuɗin fansa ko makamantansu zai fuskanci hukunci kamar yadda doka ta tanada.

Rundunar ta buƙaci al’umma su ci gaba da kasancewa cikin shiri tare da kai rahoton duk wani kira ko motsi da suke zargi ga ofishin ‘yan sanda mafi kusa.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Sauran Duniya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Tantance Gaskiyar Bayanai Shi Ne Ginshiƙin Aikin Jarida Mai Nagarta – Abdulaziz
Next Post: Yobe Ta Sake Jaddada Ƙudirin Rage Mutuwar Yara

Karin Labarai Masu Alaka

Shugaban Kasar Uganda Yana Kokarin Mayar Da Mulkin Kasar Na Gado Labarai
ECOWAS Ta Saka Dokar Ta Baci A Afrika Ta Yamma Afrika
Akwai Yiwuwar Farashin Mai Zai Kara Tashi Afrika
Tattaunawar Nukiliya Tsakanin Iran Da Amurka Yana Tasirin Akan Farashin Albarkatun Mai Amurka
Gwamnatin Tarayya Ta Ce Babu Musguna Wa ’Yan Jarida A Mulkin Tinubu Labarai
Jamhuriyar Nijar Ta Fitar Da Doka Domin Kare ‘Yancin ‘Yan Kasar Tsaro

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • APC: Tinubu Da Shettima Za Su Sake Neman Wa’adi Na Biyu A 2027
  • Sabuwar Sakatariyar Ƙungiyar Gwamnonin Arewa Za Ta Ƙarfafa Ayyukan Ci Gaban Yankin
  • TIC Dutse Ta Nemi Ƙarin Tallafin Gwamnatin Jigawa Don Faɗaɗa Ayyukanta
  • Gobara Ta Lalata Babban Zauren Majami’ar ECWA Gospel A Gombe
  • Gombe: ‘Yan Sanda Sun Tarwatsa Ƙungiyar Masu Fashi Da Damfara Ta Yanar Gizo

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Kasar Habasha Da Turkiyya Sun Kulla Yarjejeniyar Makamashi Afrika
  • CAF Ta Ci Tarar Ƙasar Masar Dala 5,000 AFCON 2025 Wasanni
  • Kungiyar ‘Yan Jarida Ta Najeriya Ta Tabbatar Da Kyautata Rayuwar Mambobin ta Labarai
  • Za’a Ninka Shekarun Zama A Gidan Kurkuku Ga Masu Auren Jinsi A Senegal Afrika
  • Rangadin Ayyukan Tinubu Ya Kai Tawaga Zuwa Kano Northern Bypass Afrika
  • Ahmed Gara Ya Kaddamar da Kofin Sarkin Gombe, Ya Jaddada Bunƙasa Matasa Afrika
  • Hawan Nasarawa A Jihar Kano Afrika
  • Iran Da Amurka Sun Gindayawa Juna Ka’idojin Tsagaita Wuta Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.