Hukumar yaki da cin hanci ta ICPC ta hada kai da jihohi don karfafa tasirin yaki da cin hanci daga tushe.
A taron wuni daya a Abuja, ICPC ta ce hakika kwamishinonin shari’a na jihohi na da gagarumar rawar takawa a yaki da almundaha.
Taron wanda ya samu halartar ministan shari’a Lateef Fagbemi da tsohon minista Kanu Agabi ya ja hankalin kwamishinonin da cewa lallai gwamnoni na sauraron shawarar su don haka ya dace su yi amfani da damar wajen kawo gyara.
Shugaban hukumar ta ICPC Barista Musa Adamu ya ce nadama kan biyo bayan duk jami’in da ke da alhakin gyara amma ya yi kasa a guiwa “lokacin da mu ka bar kujera ko tsufa ya same mu za mu ga abubuwan da ya dace mu yi to in kuwa ba mu yi ba tarihi ba zai yafe ma na ba.”
Kwamishinan shari’a na jihar Yobe Barista Saleh Samanja ya ce yaki da cin hanci kan samu nasara ne ba a lokaci daya ba don haka za a cimma nasara ta hanyar jajircewa.
Hakanan shi ma kwamishinan shari’a na jihar Jigawa Barista Bello Abdulkadir Fanini ya ce aikin na kwamishinonin ya na da muhimmaci wajen saita yaki da rashawa a matakin na jiha kasancewar su masana lamuran shari’a.
Hukumar ta ICPC da kan yaki cin hanci a tsakanin jami’an gwamnati, ta yi alwashin sakamakon taron ba zai zama zane kan ruwa ba.


