Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe Afrika
  • Hukumomin Bada Agaji Sun Fadakar Da Al’ummar Jihar Gombe Afrika
  • Ana Cigaba Da Shirye-Shiryen Fara Gasar Kwallon Sarakuna A Gombe Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Zata Samar Da Sabbin Dakunan Karatun Dalibai Afrika
  • Gwamnatin Tarayya Ta Cire Sharadin Rubuta UTME Ga Masu Neman Shiga Kwalejojin Ilimi Afrika

Gwamna Inuwa Yahaya ya Rusa Majalisar Zantaswa ta Jihar Gombe
Published: April 8, 2026 at 5:35 PM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: April 9, 2026

A zaman Majalisar Zantaswar jihar Gombe Karo na 53 Gwamna Inuwa Yahaya ya rusa Majalisar Zartarwa ta Jihar a yau laraba 08 Afrilun 2026

“Mun rusa majalisar zartarwa ta jiha ne don baiwa kwamishinonin mu dake da sha’awar takara a zaben 2027 dake tafe dama su cinma muradun su na siyasa. Bayan kwamishinoni Kazalika na bada umurni wa duk masu mukamai na siyasa a matakai daban daban dake sha’awar takara a zaben dake tafe da su ajiye aikin su daga nan zuwa 10th April, 2026 don cinma burin su na takara a mukaman da suke muradin nema. Ina musu godiya maras adadi sabida rawar da suka taka wajen nausa gwamnatin mu gaba cikin kusan shekaru uku da mukayi a zangon gwamnati na na biyu”

Gwamna Inuwa Yahaya biyo bayan rusa majalisar zartarwa ta jiha da yayi.

Gwamnan jihar Gombe Muhammadu Inuwa Yahaya, CON, ya rushe Majalisar Zartarwar Jihar, wanda hakan ya kawo ƙarshen wa’adin kwamishinonin da suka yi aiki a majalisar zartaswar tsawon shekaru biyu da rabi da suka gabata.

An sanar da wannar shawara ce yau Laraba yayin wani taron manema labarai da Sakataren Gwamnatin Jihar, Farfesa Ibrahim Abubakar Njodi, ya jagoranta jim kaɗan bayan zaman Majalisar Zartarwar karo na 53.

Farfesa Njodi ya bayyana cewa Gwamna Inuwa Yahaya ya umarci duk kwamishinonin su miƙa harkokin ma’aikatunsu ga manyan Sakatarori nan da ranar Juma’a, 10/04/2026, don ci gaba da shugabanci cikin kwanciyar hankali a ma’aikatun.

Farfesa Njodi ya ƙara da cewa a lokacin zaman, Gwamna Inuwa Yahaya ya miƙa godiya ga kwamishinonin saboda sadaukarwa, biyayya da jajircewarsu wajen ciyar da jihar gaba, tare da yaba musu kan rawar da suka taka a ɗaiɗaikunsu da kuma a ƙungiyance kan manufofi da shirye-shiryen da suka yi tasiri ga rayuwar al’ummar jihar.

Ya ƙara da cewa Gwamnan ya yi musu fatan alheri a harkokin da za su yi nan gaba, yana mai bayyana ƙwarin gwiwar cewa da yawa za su ci gaba da bada gudummawa mai ma’ana ga ci gaban Jihar Gombe dama ƙasa baki ɗaya.

A wani lamarin makamancin haka, Gwamnan ya umarci duk waɗanda aka naɗa a muƙaman siyasa, ciki har da mataimaka da masu riƙe da muƙaman siyasa dake son tsayawa takara a babban zaɓen 2027 mai zuwa, su yi murabus daga mukamansu ya zuwa ranar Juma’a 10/04/2026.

An ɗauki wannan matakin ne don tabbatar da gaskiya, riƙon amana da kuma bin ƙa’idoji da dokokin zaɓe.

A yayin zaman majalisar na bankwana, kwamishinonin sun yi cikakken nazari kan ayyukansu tun lokacin da aka rantsar da su, sannan suka yi nazari kan gudummawar da majalisar ta bayar ga ƙudurin ci gaba na gwamnati.

Sun yaba da muhimman ci gaban da aka samu a fannoni daban-daban na tattalin arziƙin jihar.

A ƙarshen zaman, majalisar ta kaɗa ƙuri’ar amincewa da Gwamna Inuwa Yahaya, inda ta yaba da salon jagorancinsa, da alƙiblar manufofi da jajircewarsa wajen sauya Jihar Gombe.

Sun bayyana cewa a ƙarƙashin jagorancinsa, jihar ta shaida gagarumin ci gaba a fannin samar da ababen more rayuwa kamar kiwon lafiya, ilimi, da sauye-sauyen tattalin arziki da sauransu, wanda hakan ya sanya Gombe ta zama jihar da ake samun ci gaba a fannin shugabanci a Najeriya.

Kwamishinonin masu barin gado sun nuna matuƙar godiya ga Gwamnan bisa damar da ya ba su na yiwa jihar hidima a irin wannan mataki, inda suka bayyana wa’adin aikinsu a matsayin mai tasiri da armashi, suna masu cewa suna alfahari da bada gudummawa ga nasarorin da gwamnatin ta samu.

Sun yi alƙawarin ci gaba da biyayya da goyon bayansu ga Gwamnan da kuma hangen nesansa na mayar da Jihar Gombe mai arziki da wadata, ko da kuwa sun koma ga harkoki na ƙashin kansu.

A lokacin taron manema labaran, Sakataren Gwamnatin ya isar da godiyar gwamna Inuwa Yahaya ga manema labarai bisa rawar da suke takawa a matsayin abokan hulɗar ci gaba da kuma goyon bayan da suke bayarwa wajen tallata manufofi da shirye-shiryen wannar gwamnatin.

Labarai, Najeriya, Siyasa

Post navigation

Previous Post: Rundunar Sojin KTK Ta Harba Makami Teku
Next Post: Kasashen Amurka,Israela Da Iran Sun Amince Da Dakatar Da Yaki

Karin Labarai Masu Alaka

Kasar India Ta Sayi Iskar Gas Daga Iran Labarai
Kasar Sham Ta Sallami Wasu Fararen Hula Labarai
Jami’an Tsaron Pakistan Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Labarai
‘Yan Majalisar Wakilai 17 Sun Fice Daga ADC Afrika
Shugaban Amurka Yayi Barazanar Kulle Wani Dan Jarida Amurka
Hukumar ‘Yan Sanda Ta Bukaci Jama’ar Jos Ta Arewa Su Rika Bin Doka Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe
  • Hukumomin Bada Agaji Sun Fadakar Da Al’ummar Jihar Gombe
  • Ana Cigaba Da Shirye-Shiryen Fara Gasar Kwallon Sarakuna A Gombe
  • Gwamnatin Najeriya Zata Samar Da Sabbin Dakunan Karatun Dalibai
  • Gwamnatin Tarayya Ta Cire Sharadin Rubuta UTME Ga Masu Neman Shiga Kwalejojin Ilimi

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Wani Dan Bindiga Ya Harbi Dakarun Tsaron Cikin Gida Su Biyu A Washington DC Labarai
  • Hukumar ICPC Ta Kwato Makudan Kudade Rediyo
  • Shugaba Trump Yace Amurka Ce Zata Rika Gudanar Da Harkokin Kasar Venezuela Amurka
  • Hare Hare A Kasar Congo Ya Jikkata Mutane Da Dama Afrika
  • Nnamdi Kanu Zai Daukaka Kara Har Zuwa Kotun Koli Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • FIFA Na Shirin Fadada Babban Na’urar VAR A Gasar Cin Kofin Duniya 2026. Wasanni
  • Kungiyar MDD Ta Bukaci Ayi Bincike Game Da Kashe ‘Yan Iran Sauran Duniya
  • Hadakar Gwamnatin Najeriya Da Amurka Ne Suka Kai Hari Sokoto Najeriya
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.