Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • PDP Ta Tsayar da Goodluck Jonathan Takarar Shugaban Kasa Afrika
  • Hawan Gidan Gwamnati A Jihar Gombe Afrika
  • Hawan Babbar Sallah A Masarautar Kaltungo Dake Jihar Gombe Afrika
  • Sarkin Gombe Ya Yabi Nasarorin Inuwa Yahaya A Fannonin Tsaro Da Raya Kasa Afrika
  • Tinubu Ya Jaddada Aniyar Rage Tsadar Rayuwa Da Samar da Ayyukan Yi Afrika

‘Yan Bindiga Sun Kashe Fiye Da Mutane 50 Tare Da Sace Mata Da Yara A Jihar Zamfara
Published: February 21, 2026 at 5:22 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

A kalla mutane 50 ne suka rasa rayukansu sakamakon harin da ‘yan bindiga suka kai wani kauye a jihar Zamfara, tare da sace mata da yara da yawa, a cewar wani dan majalisa da ya zanta da kamfanin dillancin labarai na Reuters a jiya Jumu’a.

Hamisu A Faru, dan majalisa mai wakiltar Bukkuyum ta kudu ya ce, ‘yan ta’addan sun far ma kauyen Tungan Dutse wajen karfe biyar na yamma ranar Alhamis, suka ci gaba da tafka barna har zuwa 3:30 na wayewar safiyar Jumu’a, inda suka kokkona gidaje, suka kuma rika harbin mutanen da ke guduwa don tsira da ran su.

Ya ce har yanzu ba’a san adadin mutanen da aka sace ba.

Wani mazaunin wurin Abdullahi Sani, ya ce kwana daya kafin faruwar abun mazauna kauyen sun tuntubi jami’an tsaro lokacin da suka ga babura fiye da 150 dauke da mutane, amma babu abin da aka yi a kai.

Najeriya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Kotun Amurka Ta Soke Harajin Fito Da Shugaba Trump Ya Kakabawa Kayan Kasashen Waje
Next Post: Fiye Da Mutane Miliyan Hudu Suna Fuskantar Barazanar Yunwa A Somaliya

Karin Labarai Masu Alaka

Shugaba Putin Ya Bukaci Kawo Karshen Yaki Da Iran Afrika
Iran Ta Bukaci Duniya Ta Shirya Domin Fuskantar Tsadan Mai Amurka
Rasha Takai Hari Ukraine Da Jirgi Marar Matuki Afrika
Al’ummar Jihar Nasarawa Suna Cecekuce Bisa Tsaida Aliyu Wadada Takarar Gwamna Afrika
Ankara Kai Wani Harin Bom Birnin Maiduguri Afrika
Ankara Gano Wani Abu Mai Kama Da Abun Fashewa A Jabo Jihar Sokoto Tsaro

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • PDP Ta Tsayar da Goodluck Jonathan Takarar Shugaban Kasa
  • Hawan Gidan Gwamnati A Jihar Gombe
  • Hawan Babbar Sallah A Masarautar Kaltungo Dake Jihar Gombe
  • Sarkin Gombe Ya Yabi Nasarorin Inuwa Yahaya A Fannonin Tsaro Da Raya Kasa
  • Tinubu Ya Jaddada Aniyar Rage Tsadar Rayuwa Da Samar da Ayyukan Yi

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Turkiyya Ta Zargi Alakar Isra’ila Da Somaliya Afrika
  • Rundunan  ‘Yan Sandan Jihar Bauchi, Ta Miƙa Miyagun Ƙwayoyi Da Ta Kama Wa NDLEA. Labarai
  • Gwamnatin Tarayya Ta Ce Babu Musguna Wa ’Yan Jarida A Mulkin Tinubu Labarai
  • Rwanda Zata Janye Dakaru Daga Mozambique Afrika
  • Yaki Ta Sararin Samaniya Ya Cigaba Tsakanin Amurka, Isra’ila Da Iran Afrika
  • An Bukaci Mabiya Addinin Kirista Da Suyi Koyi Da Rayuwar Yesu Najeriya
  • Koriya Ta Arewa Ya Goyi Bayan Iran Wajen Zaben Sabon Jagora Mojtaba Khameni Afrika
  • Kasar Faransa Ta Karyata Cire Afirka Ta Kudu Daga G7 Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.