Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Rundunar ‘Yan Sandan Gombe Ta Kuɓutar da Yaro Daga Hannun Masu Garkuwa Afrika
  • Tinubu Ya Buɗe Katafaren Kamfanin Sarrafa Lithium Domin Bunƙasa Tattalin Arziki Afrika
  • Sojoji Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 1,597, Sun Ceto Mutane 1,516 – DHQ Afrika
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u Afrika
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa Afrika

Tinubu Ya Aika Manyan Hafsoshin Tsaro Borno
Published: March 17, 2026 at 9:28 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu ya nuna alhininsa game da sabon harin ta’addanci da aka kai birnin Maiduguri na jihar Borno, inda ya bayyana lamarin a matsayin abin bacin rai da ban takaici.

Cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Talata, 17 ga watan Maris, 2026, Shugaba Tinubu ya jajantawa mutanen da suka rasa rayukansu da kuma wadanda suka jikkata, yana mai jaddada cewa gwamnati na tare da jama’ar Jihar Borno a wannan mawuyacin lokaci.

Shugaban ya bayyana cewa wadannan hare-hare na nuna alamun fargaba da matsin lamba da ’yan ta’addan ke fuskanta daga dakarun tsaron Najeriya.
“Wadannan ayyukan ta’addanci yunƙuri ne na ƙarshe na matsananciyar fargaba da waɗannan masu laifin ke yi domin dasa tsoro a zukatan mutane, sakamakon irin luguden wutar da suke fuskanta daga jami’anmu.” Inji Tinubu

Tinubu ya ƙara da cewa, a taron tsaro da ya gudanar a ƙarshen makon jiya, ya amince da samar da ƙarin kayan aiki da tallafin ayyuka ga hukumomin tsaro domin ƙarfafa dabarunsu na yaƙi da ta’addanci.

Domin tabbatar da an magance lamarin cikin gaggawa, Shugaba Tinubu ya ba wa manyan hafsoshin tsaro na ƙasa umarnin gaggawa na su koma birnin Maiduguri domin jagorantar ayyukan tsaro da kansu.

Haka kuma, ya umarci hukumomin agajin gaggawa da su tabbatar da sun ba wa duk waɗanda suka jikkata kulawar da ta dace.

A ƙarshe, Shugaban ya jaddada cewa babu wani lungu a Najeriya da zai zama wurin buya ga ’yan ta’adda, inda ya ce, “Ba za mu taba mika wuya ga tsoro ba. Za mu nemo su, mu fuskance su, kuma mu murƙushe su baki ɗaya.”

Afrika, Labarai, Najeriya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Lauyoyi Sun Gurfanar Da Wani A Kotu Bisa Fasa Korin Kiyashi A Kenya
Next Post: Tinubu, Akpabio da Ministoci 9 Zasu Tafi Ƙasar Birtaniya

Karin Labarai Masu Alaka

Kotu A Kasar Uganda Ta Bada Belin ‘Yar Gwagwarmaya Afrika
Zanga-Zangar Adawa Da Harin Amurka Da Isra’ila Ya Zamo Tarzoma A Pakistani Afrika
China Ta Yi Kira Da Kasashen Gabas Ta Tsakiya Su Hada Kai Labarai
Afirka Ta Kudu Ta Kubutar Da ‘Yan Kasar Da Suke Taya Sojojin Rasha Yaki Afrika
An Hana Yada Rahotannin Siyasa A Kasar Uganda Tsaro
Rundunar Wanzar Da Zaman Lafiya Zata Tabbatar Da Tsagaita Wuta A Kwango Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Rundunar ‘Yan Sandan Gombe Ta Kuɓutar da Yaro Daga Hannun Masu Garkuwa
  • Tinubu Ya Buɗe Katafaren Kamfanin Sarrafa Lithium Domin Bunƙasa Tattalin Arziki
  • Sojoji Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 1,597, Sun Ceto Mutane 1,516 – DHQ
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Tinubu Ya Nada Shugabannin Hukumar NERC Najeriya
  • Sojojin Faransa Sun Karyata Zargin Bobi Wine Labarai
  • An Kubutar Da Wani Wanda Mahaifinsa Ya daure Da Sarka Tsawon Shekaru 17 A Bauchi Labarai
  • ‘Yan Agajin Izalar Jos Sunyi Hatsari Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Za A Cigaba Da Tattaunawa Domin Kawo Karshen Yakin Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Jamhuriyar Dimokraɗiyya Kwango Zata Karbi ‘Yan Gudun Hijirar Da Amurka Ta kora Afrika
  • Gwamnatin Gombe Ta Kulla Yarjejeniyar Da New Zealand Kimiya
  • Gombe Ta Ƙaddamar da Allurar Rigakafin HIV Ta LEN PrEP Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.