Da alamun za’a ci gaba da shawarwari domin kawo karshin yakin hadin guiwar Amurka da Isra’ila akan Iran a Pakistan, cikin kwanaki masu zuwa, shugaban Amurka Donald Trump ne ya bayyana haka a ranar talata, bayan da aka kasa cimma matsaya a zaman farko, wanda ya sa Amurka ta killace tashoshin ruwan Iran.
Jami’ai daga yankin Gulf, da Pakitan da Iran suka ce tawagar wakilai daga kasashen biyu sai tayu su koma Pakistan a cikin makon nan, koda yake wani babban jami’i a Iran yace ba’a tsaida rana ba.
Yayinda killace tashoshin ruwan Iran ya janyo zazzafar magana daga Iran, alamun cewa ana ci gaba da daukar matakan difilomasiyya ya kawo nitsuwa a kasuwannin mai, har farashin mai yayi kasa da dala dari kan ko wace ganga a cinikin talatar nan.
Shawarwari tsakanin kasashen biyu masu gaba da juna da ya kunshi manyan jami’ai daga Washington da Tehran irinsa na farko, tun bayan juyin juya hali na Iran a shekara ta 1979, bai samar da ma fita ba, wanda ya janyo shakku kan makomar yarjejeniyar tsagaita wuta na mako biyu, wanda saura mako daya ya kare.


