Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro Labarai
  • Za A Cigaba Da Tattaunawa Domin Kawo Karshen Yakin Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Ministocin Kasar Asia Zasu Gudanar Da Taro A Kasar Malaysia
Published: December 22, 2025 at 9:32 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Ministocin harkokin wajen Kungiyar Kasashen yankin Kudu Maso Gabashin Asiya, zasu gana yau litinin a kasar Malaysia, da zummar kawo karshen yakin bakin iyakar da ya kashe mutane akalla 40 tare da raba mutane fiye da rabin miliyan da gidajensu cikin wannan wata a tsakanin Thailand da Cambodia.

Ministocin zasu yi kokarin farfado da shirin tsagaita wutar da aka yi aiki da shi na dan kankanin lokaci, wanda Malaysia mai rike da kujerar shugabancin kungiyar da kuma shugaba Donald Trump na Amurka suka kulla a tsakanin kasashen biyu.

Kasashen Thailand da Cambodia, wadanda su ma membobin wannan kungiya ne da ake kira ASEAN a takaice, zasu halarci taron na yau a kuala Lumpur, wannan zai zamo ido hudu na farko da jami’an kasashen biyu zasu yi da juna tun sake barkewar fada a ranar 8 ga watan nan na Disamba.

A bayan wannan yunkuri da kasashen yankin ke yi, Amurka da kasar China su ma kowacce tana nata kokarin na ganin an samu zaman lafiya a bakin iyakar kasashen biyu, amma har yanzu babu wata alama ta wanzuwar zaman lafiya.

Tsaro

Post navigation

Previous Post: Yau Litinin Ake Cigaba Da Shari’ar Najib Zarak
Next Post: Najeriya Tayi Asarar Kusan Naira Triliyan 1 Sakamakon Harajin Trump

Karin Labarai Masu Alaka

EFCC Ta Tsare Tsohon Minista Abubakar Malami Tsaro
‘Yan Sanda Sun Kama Masu Garkuwar da Mutane a Jihar Gombe Tsaro
Jamhuriyar Nijar Ta Fitar Da Doka Domin Kare ‘Yancin ‘Yan Kasar Tsaro
Rundunar Sojin Najeriya Ta Dakile Harin ‘Yan Ta’adda A Jihar Borno Labarai
Ukraine Ta Tura Tawagar Kwarerru Zuwa Kasashen Larabawan Domin Basu Kariya Labarai
‘Yan Uwa Musulmi A Jihar Gombe Sunyi Allah Wadai Da Kisan Ayatollah Khomeini Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jami’yar ADC A Najeriya Ta Kori Nafiu Bala
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro
  • ‘Yan Sanda Sun Kama Mutane 33 Bisa Zargin Kai Hari A Jihar Kwara
  • Papa Roma Leo Yayi Gargadi Game Da Rushewar Dimokraɗiyya
  • Jiragen Ruwa Suna Biyayya Ga Dokar Hana Ketare Ruwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Gwamnatin Kasar Guinea Ta Soke Wasu Jam’iyyun Siyasa Afrika
  • Sallah Sai Ranar Juma’a A Najeriya: Fadar Sarkin Musulmi Afrika
  • Yau Lahadi Ake Gudanar Da Zabe A Kasar Myanmar Labarai
  • ‘Yan Sanda Sun Kama Mutane Takwas Da Ake Zargi Da Siyar Da Tikitin AFCON Ba Bisa Ka’ida Ba Wasanni
  • Shirin Safe 0500 UTC Yau Asabar 11.15.2025 Rediyo
  • Venezuela Ta Sako Karin Mutanen Da Take Tsare Dasu Labarai
  • Ana Zargin Tsohon Shugaban Kasar Philippines Da Ta’addaci A Lokacin Mulkinsa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Bauchi: Ba Zamu Bude Makarantu Ba Sai 2026 Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.