‘Yan tawayen Houthi na Yemen sun kai wa Isra’ila hari a Karon farkon a Yau Asabar, tun bayan barkewar yaki tsakanin Amurka da Isra’ila da kuma Iran a gefe daya.
Da yake magana kafin ‘yan Houthi su kai harin, sakataren harkokin wajen Amurka, Marco Rubio, yace ana sa ran Amurka zata kammala yakin cikin makonni, amma ‘yan Houthi sun ce zasu ci gaba da kai hare-haren su, har sai kowanne bangare ya tsagaita wuta.
Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian ya zanta da prime ministan Pakistan Shebaz Sharif, wanda gwamnatin sa ta karbi bakuncin ganawa da ministocin waje na kasashen Turkiyya da Saudiyya, don neman kawo sauki ga rikicin.


