Tawaga daga Gwamnatin Jihar Benue, ƙarƙashin jagorancin Mataimakin Gwamnan jihar, tare da tawagar Ƙungiyar Makiyaya ta Najeriya (MACBAN) wadda Sakataren ƙungiyar na Kasa ya jagoranta, sun kai ziyarar ta’aziyya ga iyalan marigayi Alhaji Ardo Risku Mohammed, tsohon Shugaban MACBAN na Jihar Benue.

Tawagogin sun kai ziyarar ne domin jajanta wa iyalan marigayin, ‘yan uwansa da al’ummar yankinsa bisa rasuwarsa mai ban tausayi. Sun kuma yi addu’ar Allah Maɗaukakin Sarki Ya gafarta masa kura-kuransa, Ya yalwata masa rahama, Ya sanya shi cikin Aljannatul Firdausi, tare da bai wa iyalansa, ‘ya’yan ƙungiyar MACBAN da daukacin al’umma haƙurin jure wannan babban rashi.

A yayin ziyarar, tawagogin sun jaddada muhimmancin tabbatar da adalci, zaman lafiya da haɗin kan al’umma. Sun buƙaci iyalan marigayin da su kasance masu haƙuri da juriya, tare da tabbatar musu cewa za a ci gaba da ƙoƙarin ganin an tabbatar da adalci da kuma samar da zaman lafiya mai ɗorewa.
Haka kuma, tawagogin sun bayyana cewa rasuwar marigayi Alhaji Ardo Risku Mohammed babban rashi ne ga iyalansa, ƙungiyar MACBAN da ma al’ummar Jihar Benue baki ɗaya.


