Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama Afrika
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara Afrika
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe Afrika
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro Afrika
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa Afrika

Isra’ila Zata Karbi Mutanenta A Yankin Gaza
Published: December 29, 2025 at 10:34 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Ana samun karin kasashen dake fitowa suna yin Allah wadarai da amincewar da kasar Isra’ila ta yi da yankin Somaliland na kasar Somaliya a zaman kasa mai ‘yanci.

Ba a san dalilin da ya sa isra’ila ta fito ranar Jumma’a tana fadin cewa ta amince da Somaliland a zaman ‘yan tacciyar kasa ba, amma kuma a farkon shekarar nan jami’an Amurka da na Isra’ila sun fada ma kamfanin dillancin labarai na Associated Press cewa Isra’ila ta tuntubi jami’an yankin na Somaliland, a kan ko zasu karbi Falasdinawa na yankin Gaza, a wani bangare na shirin Shugaba Trump a wancan lokaci na sake tsugunar da mutanen Gaza a wani wuri kuma tuni dai Amurka ta yi watsi da wancan shirin nata.

Wata sanarwar hadin guiwar da kasashe fiye da 20 tare da kungiyar kasashen Musulmi ta duniya OIC suka bayar ta yi watsi da wannan amincewa da isra’ila ta ce ta yi da yankin na Somaliland a zaman kasa mai cin gashin kai, ganin irin yadda hakan zai yi mummunar barazana ga zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin.

Yankin Somaliland ya bayyana ballewa daga Somaliya tun shekarar 1991, amma duk da cewa yana da gwamnati da takardar kudin sa daban, babu wata kasa a duniya da ta taba yarda da shi a zaman kasa.

Sanarwar kasashen ta kuma nuna rashin yarda ko miskala zarratin, da duk wani matakin da Isra’ila zata ce zata dauka dangane da wannan, wajen korar Falasdinawa karfi da yaji daga gidaje da garuruwa da yankunan su.

Ita ma kasar Sham, ko Syria, tayi tur da wannan mataki na Isra’ila a wata sanarwa dabam da ta bayar.

A ranar asabar, ma’aikatar harkokin wajen Amurka ta fitar da sanarwa tana jaddada ci gaba da mutunta kasar Somaliya wadda yankinta ya hada da yankin na Somaliland.

Gwamnatin tarayyar Somaliya ta fito ran jumma’a da kakkausar harshe tana yin tur da wannan matakin na Isra’ila da ta ce haramun ne.

Shi ma shugaban Kungiyar Tarayyar Kasashen Afirka, Mahmoud Ali Youssouf, yace duk wani matakin gurgunta diyaucin Somaliya na iya haddasa fitina a nahiyar.

Labarai

Post navigation

Previous Post: Anfara Kirga Kuri’a A zaben Kasar Guinea
Next Post: Ana Cigaba Da Tattaunawa Tsakanin Trump Da Zelensky Domin Tsagaita Wuta A Ukraine

Karin Labarai Masu Alaka

Isra’ila Tace Bazata Sake Kai Hari Kan Cibiyar Gas Ta Iran Ba Afrika
Ansamu Girgizar Kasa A Kasar Taiwan Labarai
Majalisar Dokokin Filato Ta Kare Kudirin Alawus Ga Tsofaffin ‘Yan Majalisa Afrika
Yaki Tsakanin Rasha Da Ukraine Yayi Ajalin ‘Yan Ghana 50 Afrika
Rundunar Tsaron Haɗin Gwiwa Ta Arewa Maso Gabas Ta Kashe Fiye Da ‘Yan Ta’adda 438 Labarai
Kasar Malawi Ta Kaddamar Da Rigakafin Shan Inna Kiwon Lafiya

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Chelle: Rashin Jituwa Tsakanin Osimhen Da Lookman Matsala Ce Ta Cikin Gida Wasanni
  • Gwamna Abba Ya Gana Da Kwankwaso Kamun Ganawarsa Da Tinubu Siyasa
  • Jami’ai A Mexico Sun Tabbatar Da Kashe Shugaban Masu Shan Ƙwaya Nemesio Oseguera Labarai
  • Kauran Gwandu Zai Inganta Wutan Lantarki A Kebbi Siyasa
  • Gwamnatin Soji A Nijar Ta Hana Fitar Da Albarkatun Kasa Afrika
  • Rundunan  ‘Yan Sandan Jihar Bauchi, Ta Miƙa Miyagun Ƙwayoyi Da Ta Kama Wa NDLEA. Labarai
  • Majami’ar Anglican Zasuyi Taron Zaben Sabon Shugaba Afrika
  • Okoye Na Shirin Maye Gurbin Nwabali, AFCON 2025: Wasanni
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.