Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro Labarai
  • Za A Cigaba Da Tattaunawa Domin Kawo Karshen Yakin Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Gwamna Abba Ya Gana Da Kwankwaso Kamun Ganawarsa Da Tinubu
Published: January 11, 2026 at 1:50 PM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: January 11, 2026

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya gudanar da wata ganawar sirri da jagoran jam’iyyar NNPP kuma tsohon gwamnan jihar, Rabiu Musa Kwankwaso, a gidansa da ke Miller Road, Kano, gabanin tafiyarsa zuwa ƙasar Faransa domin ganawa da shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu.

Rahotanni sun nuna cewa ganawar ta gudana ne a daren Talata, 6 ga Janairu, 2026. Majiyoyi sun bayyana cewa gwamnan ya isa gidan Kwankwaso da tsakar dare, cikin wata mota mai duhu.

Majiyoyi sun ce tattaunawar ta ɗauki sama da awa guda, amma bayanai sun nuna cewa gwamnan bai samu nasarar shawo kan Sanata Kwankwaso ba domin ya bi shi zuwa jam’iyyar APC, kamar yadda ake zargin akwai matsin lamba daga wasu manyan mutane.

Bayan kammala ganawar, washe gari, Sanata Kwankwaso ya yi jawabi ga magoya bayansa a gidansa, inda ya jaddada cewa ba shi da “farashi” a siyasa kuma yace cin amana ba abu ne mai kyau ba, yana mai nuni da matsalolin tsaro da tattalin arziki da ke rage farin jinin jam’iyyar APC a idon jama’a.

“Wasu na cewa a Nijeriya kowa na da farashi. Idan kana neman wanda ba shi da farashi, ka zo wurin Rabiu Kwankwaso,” in ji shi.

Rahoton ya ce shirin gwamnan na sauya sheƙa zuwa APC ya fuskanci cikas bayan shugabannin jam’iyyar sun lura da martanin jama’ar Kano, Duk da cewa wasu ‘yan majalisar dokoki na NNPP a matakin jiha da ƙasa, da kuma wasu shugabannin ƙananan hukumomi, na shirin sauya sheƙa tare da gwamnan, mafi yawan magoya bayan NNPP a jihar sun ci gaba da nuna cikakken goyon baya ga Kwankwaso.

Wata majiya ta bayyana cewa shugabannin APC na sa ido sosai kan halin da ake ciki a Kano, inda magoya bayan Kwankwasiyya ke nuna karara cewa suna tare da Kwankwaso.

Majiyar ta ce idan gwamnan ya shiga APC, akwai yiwuwar ɗan takarar da Kwankwaso ya goyi baya ya samu ƙuri’u masu yawa sakamakon ramuwar gayya.

Majiyoyi sun kuma ce Shugaban kasa na ci gaba da yunƙurin ganin Kwankwaso ya shiga APC, abin da ya sa ake neman shawo kansa ta hanyoyi daban-daban.

Rahoton ya ƙara da cewa ana sa ran gwamnan zai gabatar wa Shugaban kasa cikakken bayani kan sakamakon ganawarsa da Kwankwaso, tare da tsara matakan tafiyar da al’amuran jam’iyya idan ya yanke shawarar sauya sheƙa.

A halin yanzu, manyan shugabannin APC a Kano, ciki har da tsohon gwamna Abdullahi Ganduje, mataimakin shugaban majalisar dattawa Barau Jibrin, shugaban jam’iyyar APC na jiha Abdullahi Abbas, da Nasiru Gawuna da Murtala Garo, sun dawo ƙasar nan bayan hutun ƙarshen shekara da aikin Umrah.

Ana sa ran Gwamna Abba Kabir Yusuf zai sanar da matsayinsa kan batun sauya sheƙa ne bayan kammala shawarwari da shugabannin APC a jihar.

Siyasa

Post navigation

Previous Post: Wikki Tourist FC: Ta Sallami ‘Yan Wasa Hudu
Next Post: Habasha Tafara Gina Filin Jirgin Sama Mafi Girma A Afirka

Karin Labarai Masu Alaka

Prime Ministan Senegal Ya Bayyana Shirin Sauya Sheka Afrika
Shugaban Amurka Yayi Watsi Da Tattaunawar Kawo Karshen Yaki Da Iran Afrika
Ministan Harkokin Wajen Najeriya Yayi Murabus Afrika
Gwamnatin Tinubu Zata Gyara Hanyar Akwanga Zuwa Jos Labarai
Aminu Tambuwal Ya Fice Daga PDP Ya Koma ADC Afrika
Gwamnatin Sojan Burkina Faso Ta Soke Jam’iyyun Siyasar Kasar Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jami’yar ADC A Najeriya Ta Kori Nafiu Bala
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro
  • ‘Yan Sanda Sun Kama Mutane 33 Bisa Zargin Kai Hari A Jihar Kwara
  • Papa Roma Leo Yayi Gargadi Game Da Rushewar Dimokraɗiyya
  • Jiragen Ruwa Suna Biyayya Ga Dokar Hana Ketare Ruwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • China Ta Dawo Da Harajin Magungunan Hana Haihuwa Labarai
  • Darajar Kudin Afirka Ta Kudu Ya Tashi Afrika
  • Anyi Taho Mugama Tsakanin ‘Yan Sandan Turkiyya Da ‘Yan Kungiyar ISIS Afrika
  • Shugaba Tinubu Ya Isa Legas Domin Hutun Karshen Shekara Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Shugaban Kasar Uganda Yana Kokarin Mayar Da Mulkin Kasar Na Gado Labarai
  • Ana Cigaba Da Samun Hare Hare Da Jiragen Marasa Matuki A Sudan Labarai
  • An Kaddamar Da Kwamitin Kwallon Kafa A Tsakanin Masarautun Jihar Gombe Labarai
  • Zabebben Shugaban Hungary Yace Zaidawo Da Tsarin Dimokraɗiyya Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.