Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Gwamna Abba Ya Gana Da Kwankwaso Kamun Ganawarsa Da Tinubu
Published: January 11, 2026 at 1:50 PM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: January 11, 2026

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya gudanar da wata ganawar sirri da jagoran jam’iyyar NNPP kuma tsohon gwamnan jihar, Rabiu Musa Kwankwaso, a gidansa da ke Miller Road, Kano, gabanin tafiyarsa zuwa ƙasar Faransa domin ganawa da shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu.

Rahotanni sun nuna cewa ganawar ta gudana ne a daren Talata, 6 ga Janairu, 2026. Majiyoyi sun bayyana cewa gwamnan ya isa gidan Kwankwaso da tsakar dare, cikin wata mota mai duhu.

Majiyoyi sun ce tattaunawar ta ɗauki sama da awa guda, amma bayanai sun nuna cewa gwamnan bai samu nasarar shawo kan Sanata Kwankwaso ba domin ya bi shi zuwa jam’iyyar APC, kamar yadda ake zargin akwai matsin lamba daga wasu manyan mutane.

Bayan kammala ganawar, washe gari, Sanata Kwankwaso ya yi jawabi ga magoya bayansa a gidansa, inda ya jaddada cewa ba shi da “farashi” a siyasa kuma yace cin amana ba abu ne mai kyau ba, yana mai nuni da matsalolin tsaro da tattalin arziki da ke rage farin jinin jam’iyyar APC a idon jama’a.

“Wasu na cewa a Nijeriya kowa na da farashi. Idan kana neman wanda ba shi da farashi, ka zo wurin Rabiu Kwankwaso,” in ji shi.

Rahoton ya ce shirin gwamnan na sauya sheƙa zuwa APC ya fuskanci cikas bayan shugabannin jam’iyyar sun lura da martanin jama’ar Kano, Duk da cewa wasu ‘yan majalisar dokoki na NNPP a matakin jiha da ƙasa, da kuma wasu shugabannin ƙananan hukumomi, na shirin sauya sheƙa tare da gwamnan, mafi yawan magoya bayan NNPP a jihar sun ci gaba da nuna cikakken goyon baya ga Kwankwaso.

Wata majiya ta bayyana cewa shugabannin APC na sa ido sosai kan halin da ake ciki a Kano, inda magoya bayan Kwankwasiyya ke nuna karara cewa suna tare da Kwankwaso.

Majiyar ta ce idan gwamnan ya shiga APC, akwai yiwuwar ɗan takarar da Kwankwaso ya goyi baya ya samu ƙuri’u masu yawa sakamakon ramuwar gayya.

Majiyoyi sun kuma ce Shugaban kasa na ci gaba da yunƙurin ganin Kwankwaso ya shiga APC, abin da ya sa ake neman shawo kansa ta hanyoyi daban-daban.

Rahoton ya ƙara da cewa ana sa ran gwamnan zai gabatar wa Shugaban kasa cikakken bayani kan sakamakon ganawarsa da Kwankwaso, tare da tsara matakan tafiyar da al’amuran jam’iyya idan ya yanke shawarar sauya sheƙa.

A halin yanzu, manyan shugabannin APC a Kano, ciki har da tsohon gwamna Abdullahi Ganduje, mataimakin shugaban majalisar dattawa Barau Jibrin, shugaban jam’iyyar APC na jiha Abdullahi Abbas, da Nasiru Gawuna da Murtala Garo, sun dawo ƙasar nan bayan hutun ƙarshen shekara da aikin Umrah.

Ana sa ran Gwamna Abba Kabir Yusuf zai sanar da matsayinsa kan batun sauya sheƙa ne bayan kammala shawarwari da shugabannin APC a jihar.

Siyasa

Post navigation

Previous Post: Wikki Tourist FC: Ta Sallami ‘Yan Wasa Hudu
Next Post: Habasha Tafara Gina Filin Jirgin Sama Mafi Girma A Afirka

Karin Labarai Masu Alaka

Kasar Zimbabwe Ta Samar Da Dokar Tsawaita Mulkin Mnangagwa Zuwa 2030 Labarai
INEC: Akwai Yiwuwar Dage Zaben 2027 Saboda Azumi Labarai
An Kaddamar Da Rijistar Zamani Ta Zamowa Mamba A Jam’iyar APC Siyasa
Take Hakkin Dan Adam Zai Haifar Da Juyin Juya Hali A Najeriya Najeriya
Gwamnatin Tarayya Na Kokarin Hana Demokraɗiyya A Najeriya Siyasa
Mutane Da Dama Sun Rasa Rayukansu Yayin Rikici A Uganda Siyasa

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Yakin Gabas Ta Tsakiya Ya Kawo Cikas Ga Cinikin Nama A Kenya
  • Sabon Jagoran Addinin Iran Mojtaba Khameni Yaji Rauni Kuma Ya Nakasa
  • Shugaba Trump Yace Amurka Takai Hari Kharg Tsibiri a Kasar Iran
  • MDD: Fiye Da Farar Hula Metan 200 Suka Mutu A Sudan
  • Jami’ai A Afirka Sunce Tashin Farashin Mai Kalubale Ne Ga Tattalin Arziki

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Margayi Shugaba Muhammadu Buhari 1942-2025 Labarai
  • Gwamnatin Kano Zata Dauki Mataki Game Da Kisan Dorayi Tsaro
  • Jagoran Kasar Iran Yace Basa Bukatar Tallafin Kasar Amurka Afrika
  • An Kaddamar Da Rijistar Zamani Ta Zamowa Mamba A Jam’iyar APC Siyasa
  • Gwamnatin Tarayya: Bikin Al’adun Argungu Ya Karbu A Idon Duniya Labarai
  • Shirin Dare 2030 UTC Yau Litinin 11.17.2025 Rediyo
  • An Gano Wasu Boma Bomai Da Aka Binne A Jihar Neja Najeriya
  • Tsananin Sanyi Ya Kashe Mutane 38 A Amurka Amurka
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.