Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojoji Sun Ceto Mutane 23, Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 19 A Cikin Sa’o’i 24 Afrika
  • 3G Taskforce Ya Dasa Bishiyoyi Don Kare Muhalli A Gombe Afrika
  • Builder Mahmood Yusuf Ya Tallafa Wa Mata Da Matasa Afrika
  • Gwamnan Jihar Bauchi Ya Jagoranci Tsohon Shugaban Kasar Najeriya Rangadi A Bauchi Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya Amince Da Naɗin Manyan Sakatarori 19 Afrika

Tinubu Zai Gabatar Da Jawabi ga Shugabannin Duniya A Taron UNGA
Published: July 19, 2026 at 8:37 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Shugaban Ƙasar Najeriya Bola Ahmed Tinubu, zai halarci zama na 81 na Babban Zauren Majalisar Ɗinkin Duniya (UNGA), wanda za a gudanar a birnin New York na ƙasar Amurka a watan Satumba, inda ake sa ran zai gabatar da jawabi ga shugabannin ƙasashen duniya.

Jakadan Najeriya a Majalisar Ɗinkin Duniya, Ambasada Jimoh Ibrahim, ne ya bayyana hakan bayan wata ganawa da ya yi da Shugaba Tinubu a Fadar Shugaban Ƙasa da ke Abuja.

A cewarsa, Shugaba Tinubu ya tabbatar da aniyarsa ta halartar taron tare da amincewa da dukkan shirye-shiryen da Nijeriya ta kammala domin halartar babban taron na bana.

Zama na 81 na Babban Zauren Majalisar Ɗinkin Duniya zai fara ne a ranar 8 ga watan Satumba, yayin da za a fara muhawarar shugabannin ƙasashe a mako mai zuwa.

Ana sa ran shugabannin duniya za su tattauna muhimman batutuwa da suka haɗa da sauyin yanayi, ci gaba mai ɗorewa, zaman lafiya da tsaro na duniya, da kuma sauran manyan ƙalubalen da ke fuskantar al’ummomin duniya.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Sana'o'i, Sauran Duniya, Siyasa

Post navigation

Previous Post: Gwamna Inuwa Yahaya Ya Rantsar Da Sabon Shugaban Ma’aikatan Jiha da Kwamishinoni 23
Next Post: CHAN Ta Duba Lafiyar Idanun ‘Yan Jarida A Filato

Karin Labarai Masu Alaka

Ferfesa Pantami Yasamu Tikitin Takarar Gwamnan Gombe A Jami’yar PDP Afrika
Masana Lafiya – Preeclampsia Cuta Ce Mai Hadari Amma Ana Iya Magance Ta Afrika
An Fara Dawo Da Alhazain Najeriya Gida Afrika
Sojojin Da Suka Kifar Da Farar Hula A Guinea-Bissau Sun Sanar Da Cewa! Afrika
Atiku Ya Zargi Gwamnati Da Kama ‘Yan Adawa Labarai
Kasar Gambiya Ta Gayawa Kotun MDD Shirin Myanmar Akan Musulmai Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojoji Sun Ceto Mutane 23, Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 19 A Cikin Sa’o’i 24
  • 3G Taskforce Ya Dasa Bishiyoyi Don Kare Muhalli A Gombe
  • Builder Mahmood Yusuf Ya Tallafa Wa Mata Da Matasa
  • Trump Ya Yi Gargadi Kan Shirin Cire Shugaban FIFA Infantino
  • Katsina United Ta Yi Jimamin Mutuwar Ɗan Wasanta Ozoh

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Gwamnatin Najeriya Ta Jadda Da Aniyar Rage Radadin Talauci Afrika
  • An Fara Azumin Watan Ramadan A Najeriya Da Sassan Duniya  Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Shugaba Trump Ya Yabawa Iran Bisa Bude Mashigar Hormuz Amurka
  • Najeriya Ta Bawa Dan Takarar Guinea-Bissau Mafaka Afrika
  • Ukraine Ta Aika Tawagar Kwararru Gabas Ta Tsakiya Afrika
  • Shirin Safe 0500 UTC Yau Juma’a 11.21.2025 Rediyo
  • Sakataren Tsaron Amurka Ya Kori Shugaban Sojin Kasar Amurka
  • Harin Da Israela Ta Kai Gaza Yayi Ajalin Mutane 27 Da Yara Uku Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.