Shugaban Ƙasar Najeriya Bola Ahmed Tinubu, zai halarci zama na 81 na Babban Zauren Majalisar Ɗinkin Duniya (UNGA), wanda za a gudanar a birnin New York na ƙasar Amurka a watan Satumba, inda ake sa ran zai gabatar da jawabi ga shugabannin ƙasashen duniya.
Jakadan Najeriya a Majalisar Ɗinkin Duniya, Ambasada Jimoh Ibrahim, ne ya bayyana hakan bayan wata ganawa da ya yi da Shugaba Tinubu a Fadar Shugaban Ƙasa da ke Abuja.
A cewarsa, Shugaba Tinubu ya tabbatar da aniyarsa ta halartar taron tare da amincewa da dukkan shirye-shiryen da Nijeriya ta kammala domin halartar babban taron na bana.
Zama na 81 na Babban Zauren Majalisar Ɗinkin Duniya zai fara ne a ranar 8 ga watan Satumba, yayin da za a fara muhawarar shugabannin ƙasashe a mako mai zuwa.
Ana sa ran shugabannin duniya za su tattauna muhimman batutuwa da suka haɗa da sauyin yanayi, ci gaba mai ɗorewa, zaman lafiya da tsaro na duniya, da kuma sauran manyan ƙalubalen da ke fuskantar al’ummomin duniya.


