Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Rundunar ‘Yan Sandan Gombe Ta Kuɓutar da Yaro Daga Hannun Masu Garkuwa Afrika
  • Tinubu Ya Buɗe Katafaren Kamfanin Sarrafa Lithium Domin Bunƙasa Tattalin Arziki Afrika
  • Sojoji Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 1,597, Sun Ceto Mutane 1,516 – DHQ Afrika
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u Afrika
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa Afrika

Kotun Uganda Tayi Watsi Da Karar Hukumomin Kasar
Published: February 3, 2026 at 10:09 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Wata kotu a Uganda ranar Litinin, tayi watsi da karar da hukumomin kasar suka shigar kan mutum na farko da ake tuhuma da laifin “luwadi mafi tsanani,” laifi da idan kotu ta tabbatar ana yanke masa hukuncin kisa, kamar yadda lauyan mutumin ya gayawa kamfanin dillancin labarai na Reuters.

Dokar wacce Uganda ta kafa a shekarar 2023, inda tayi kunnen kashi daga matsin lambar kasashen yammacin duniya, da kungiyoyin kare hakkin Bil’adama na gida da ketare, ana kallon dokar a zaman mafi tsanani a duniya kan ‘yan luwadi, dokar ta yi tanadin daurin rai da rai idan aka kama mutum da laifin luwadi, sannnan ta tanadi hukuncin kisa bisa wasu dalilai na musamman. Sharuddan sun hada da maimaita laifin da ake zargin mutum dashi, ko yin luwadi ga mutumin da bai balaga ba, ko ga tsoho, ko mutumin da yake dauke da wata larura.

Wanda ake tuhuman a yanzu dan shekaru 20 da haifuwa, an kama shi ne a shekara ta 2023, kan zargin yayi luwadi da wani mutum dan shekara 41 da haifuwa, wadda ya fada karkashin rukunin laifi na musamman, kamar yadda lauyansa ya fadawa kamfanin dillancin labarai na Reuters ranar talata.

Ranar Litinin, Alkali a kotun majistrate a Uganda, ya kori karar, bayanda kotu ta fahimci cewa mutumin ya sami gushewar hankali, saboda tsawon lokaci da yayi yana tsare.

Kakakin kotunan Uganda bashi da ta cewa da aka tuntube shi kan wannan shari’ar.

Afrika, Labarai

Post navigation

Previous Post: Bincike Yanuna Kasashen Afirka Suna Cikin Mafiya Cin Bashi A Duniya
Next Post: Wakilan Majalisar Dokokin Phillipines Suna Yunkurin Tsige Shugaban Kasar

Karin Labarai Masu Alaka

Shugaba Tinubu Ya Taya Musulmai Murnar Sallah, Tare Da Kira Zuwa Ga Kishin Kasa Afrika
Dakarun Gwamnatin Kasar Sham Tayi Mamaya Zuwa Gabashin Kasar Labarai
Farashin Kasuwar Yawon Bude Ido A Kasuwar Hannayen Jari Ya Fadi Afrika
Shugaba Tinubu Ya Yabawa Dakarun Tsaro Bisa Ceto Matar Marigayi Janar Rabe Afrika
Ukraine Ta Aika Tawagar Kwararru Gabas Ta Tsakiya Afrika
Kasar Israela Zata Gina Sansani A Gaza Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Rundunar ‘Yan Sandan Gombe Ta Kuɓutar da Yaro Daga Hannun Masu Garkuwa
  • Tinubu Ya Buɗe Katafaren Kamfanin Sarrafa Lithium Domin Bunƙasa Tattalin Arziki
  • Sojoji Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 1,597, Sun Ceto Mutane 1,516 – DHQ
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Shugaba Tinubu Ya Gana Da Wasu Gwamnoni Shida Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Rikicin Gabas Ta Tsakiya Yanuna Alakar Kasashen Da Najeriya Afrika
  • Amurka Ta Nuna Damuwa Kan Matsalar ‘Yan Gudun Hijira A Najeriya Najeriya
  • Mohammed Abdullahi Abubakar Ya Sayi fom Don Tsayawa Takarar kujeran Gwamnan Bauchi A APC 2027 Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ambaliyar Ruwa Yayi Ajalin Mutane A Nairobi Afrika
  • Masar Ta Kayyade Farashin Buradi A Kasar Afrika
  • Gwamnatin Gombe Zata Inganta Samar Da Wuta Wajen Amfani Da Hasken Rana Kimiya
  • Shugaban Kasar Iran Yace Kasar Bata Da Kiyayya Tsakaninta Da Amurkawa Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.