Ambaliyar ruwa ya hallaka mutane 23 a Nairobi, babban birnin kasar Kenya, ya kuma tafi da motoci da dama tare da kawo tsaiko ga zirga-zirgar jiragen sama a filin jirgin sama mafi girma a gabashin Afrika, a cewar hukumomin kasar.

Shugaban kasar Kenya, William Ruto ya ce ya aike da masu bada agajin gaggawa, ciki har da sojoji domin kawo dauki, kuma yana mika ta’aziyyar sa ga wadanda abun ya shafa.
Masana kimiyya sun ce dumamar yanayi yana kara dagula aukuwar ambaliyar ruwa da fari a gabashin Afirka. Wani bincike da aka yi a shekarar 2024 ya gano cewa sauyin yanayi ya sa ruwan sama mai yawa dake jawo ambaliya ya nunka yadda aka saba gani a yankin.


