Yunkurin samadda ‘yan sandan jihohi na kara kankama a Najeriya, tun bayan da sufeta janar na ‘yan sandan Najeriya, Olatunji Disu ya kaddamar da wani komiti mai mutane takwas da zai duba yadda za’a aiwatar da ‘yan sandan jihohi a Najeriya.
Sufetan janar na ‘yan sandan wanda ya jaddada cewa babu gudu babu ja da baya kan yin garambawul da samadda ‘yan sanda jihohi, ya kuma ce ayyukan ‘yan sandan jihohin ba zai gurgunta ayyukan ‘yan sandan Najeriya ba.
Kan haka ne, Gwamnan jahar Filato, Caleb Mutfwang shima ya kaddamar da komiti mai mutane goma sha hudu da zasu bada shawarwari kan kafa rundunar ‘yan sandan jiha don karfafa tsaro a Jihar Filato.
Gwamnan yace komitin zai yi nazari kan batun samadda ‘yan sanda a jihar bisa tsarin gwamnatin tarayya da bada shawarwari da zasu taimaka a tattaunawar da ake yi a kasa kan sauye-sauye da ake yi na samadda tsaro.
Honarabul Musa Yunusa Ayiga, tsohon mataimakin shugaban kungiyar kwadago bangaren masu samarda wutar lantarki a Najeriya yace baiwa gwamnoni damar kafa ‘yan sandan jihohi bai dace ba.
A bangare guda kuwa, Rabaran Ayuba Asheshe yace suna addu’ar Allah ya tabbatar da alheri.
Sufeta janar na ‘yan sandan Najeriya, Olatunji Disu yace kiraye-kirayen da suke samu na karfafa hanyoyin tsaro a cikin kasar, shine ya sanya su daukan matakin kaddamar da komitin da ya bashi wata guda ya gabatar da rahotonsa.
Wakiliyar GTA Hausa Amurka Ke Magana a jihar Filato Zainab Babaji ta aiko mana rahoto


