Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

Yunkurin Samar Da ‘Yan Sandan Jihohi Na Kara Kankama A Najeriya
Published: March 13, 2026 at 8:46 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Yunkurin samadda ‘yan sandan jihohi na kara kankama a Najeriya, tun bayan da sufeta janar na ‘yan sandan Najeriya, Olatunji Disu ya kaddamar da wani komiti mai mutane takwas da zai duba yadda za’a aiwatar da ‘yan sandan jihohi a Najeriya.

Sufetan janar na ‘yan sandan wanda ya jaddada cewa babu gudu babu ja da baya kan yin garambawul da samadda ‘yan sanda jihohi, ya kuma ce ayyukan ‘yan sandan jihohin ba zai gurgunta ayyukan ‘yan sandan Najeriya ba.

Kan haka ne, Gwamnan jahar Filato, Caleb Mutfwang shima ya kaddamar da komiti mai mutane goma sha hudu da zasu bada shawarwari kan kafa rundunar ‘yan sandan jiha don karfafa tsaro a Jihar Filato.

Gwamnan yace komitin zai yi nazari kan batun samadda ‘yan sanda a jihar bisa tsarin gwamnatin tarayya da bada shawarwari da zasu taimaka a tattaunawar da ake yi a kasa kan sauye-sauye da ake yi na samadda tsaro.

Honarabul Musa Yunusa Ayiga, tsohon mataimakin shugaban kungiyar kwadago bangaren masu samarda wutar lantarki a Najeriya yace baiwa gwamnoni damar kafa ‘yan sandan jihohi bai dace ba.

A bangare guda kuwa, Rabaran Ayuba Asheshe yace suna addu’ar Allah ya tabbatar da alheri.

Sufeta janar na ‘yan sandan Najeriya, Olatunji Disu yace kiraye-kirayen da suke samu na karfafa hanyoyin tsaro a cikin kasar, shine ya sanya su daukan matakin kaddamar da komitin da ya bashi wata guda ya gabatar da rahotonsa.

Wakiliyar GTA Hausa Amurka Ke Magana a jihar Filato Zainab Babaji ta aiko mana rahoto

https://gtahausa.com/wp-content/uploads/2026/03/AUD-20260313-WA0041.mp3
Labarai

Post navigation

Previous Post: An Gargaɗi Mazauna Maiduguri Su Guji Yaɗa Labaran Ƙarya
Next Post: Shugaban Amurka Donald Trump Yace Amurka Zata Kai Babban Farmaki Iran

Karin Labarai Masu Alaka

Kasashen Thailand Da Cambodia Sun Amince Da Tsagaita Wuta Labarai
Rasha Ta Gargadi Amurka Da Isra’ila Kan Harin Iran Afrika
Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro Afrika
Shugaba Yoweri Musevini Ya Zamo Shugaban Uganda Na 7 Yana Da Shekaru 81 Kuma Ya Shafe Shekaru 50 A Mulki Labarai
China Ta Yi Kira Da Kasashen Gabas Ta Tsakiya Su Hada Kai Labarai
Papa Roma Leo Yace Zai Cigaba Da Sukan Yake Yake Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Gwamnatin Najeriya Ta Samar Da Wuta Mai Aiki Da Hasken Rana A Jami’ar ADUSTECH Afrika
  • Kasar Saudiya Zata Cika Azumi Talatin Kimiya
  • Gwamna Ahmad Aliyu Na Jihar Sokoto Ya Gabatar Da Kasafin Fiye Da Naira Biliyan 700 Labarai
  • Sakataren Tsaron Amurka Ya Kori Shugaban Sojin Kasar Amurka
  • Makarantun Allo Zasu Yi Gogayya Da Na Boko Labarai
  • Ƙungiyar Mata Sunyi Kira Ga Jam’iyar P R P Da Ta Dauki Baheejja A Matsayin Mataimakiyar Gwamnan A Bauchi 2027 Labarai
  • Kasar Habasha Da Turkiyya Sun Kulla Yarjejeniyar Makamashi Afrika
  • Shugabannin Kasashen Sahel Sunyi Taro a Mali Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.