Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Rundunar ‘Yan Sandan Gombe Ta Kuɓutar da Yaro Daga Hannun Masu Garkuwa Afrika
  • Tinubu Ya Buɗe Katafaren Kamfanin Sarrafa Lithium Domin Bunƙasa Tattalin Arziki Afrika
  • Sojoji Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 1,597, Sun Ceto Mutane 1,516 – DHQ Afrika
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u Afrika
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa Afrika

Shugaban Amurka Donald Trump Yace Amurka Zata Kai Babban Farmaki Iran
Published: March 14, 2026 at 4:15 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Shugaba Donald Trump yace Amurka zata kai farmaki mai tsanani kan Iran “makon da yake zuwa,” jim kadan bayan da ya dage takunkumi kan sayen mai daga Rasha na tsawon kwanaki 30, da nufin saukaka farashin mai da yayi tashin goron zabbi, sakamakon hare-haren hadin guiwar da Amurka da Isra’ila suka kaddamr kan Iran.

Farashin mai yana kwan gaba kon baya kan canjin kalaman shugaba Trump game da tsawon lokaci da zai dauka a kammala wannan yaki, wadda yasa Iran take kai hare hare kan jiragen ruwa a mashigin ruwan Hormuz, hanyar da ake bi da kashi 1 cikin biyar na mai da duniya take amfani dashi.

A baya shugaba Trump yace “an gama yakin,” ya kuma yi alkawarin baiwa jiragen ruwan kariya a mashigin ruwan Hormuz. A hira da yayi da tashar talabijin ta FOX da tashar ta nuna jumma’an nan , Trump yace Amurka zata raka jiragen ruwan da za su bi ta mishigin ruwan “idan muka buka ci yin haka.”

Farashin mai da ake kira Brent ya sauka zuwa dala 99. da centi 80, wadda har yanzu yake nuna farashin man ya karu da kamar kashi 40 cikin dari tun fara wannan yaki.

Ahalinda ake ciki kuma jani-injaka ya turnuke a fadar White House tsakanin hadiman shugaba Trump ta hanyar da Amurka zata ayyana nasara a yaki kan Iran yayinda rikicin yake kara bazuwa a fadin gabas ta tsakiya, ganin babu wata mafita kai tsaye da Amurka zata bi ta tsaida fadan.

Afrika, Amurka, Labarai, Sauran Duniya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Yunkurin Samar Da ‘Yan Sandan Jihohi Na Kara Kankama A Najeriya
Next Post: Gabannin Harin Amurka Da Isra’ila Iran Farisa Ta Shirya Nata

Karin Labarai Masu Alaka

Hukumar Zabe Ta Saukaka Gudanar Da Rijistar Katin Zabe A Najeriya Labarai
Jami’in Diflomasiyyar Da Ake Zargi Da Kisan Prime minister Ya Daukaka Kara Afrika
Hukumar EFCC Ta Kama Dan Kasuwa A Kamaru Afrika
Shugaban Amurka Yayi Watsi Da Tattaunawar Kawo Karshen Yaki Da Iran Afrika
Darajar Kudin Afirka Ta Kudu Ya Tashi Afrika
Gwamnatin Kano Ta Samar Da Wasu Dabarun Inganta Tsaro Tsaro

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Rundunar ‘Yan Sandan Gombe Ta Kuɓutar da Yaro Daga Hannun Masu Garkuwa
  • Tinubu Ya Buɗe Katafaren Kamfanin Sarrafa Lithium Domin Bunƙasa Tattalin Arziki
  • Sojoji Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 1,597, Sun Ceto Mutane 1,516 – DHQ
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Ferfesa Pantami Yasamu Tikitin Takarar Gwamnan Gombe A Jami’yar PDP Afrika
  • Shugaban Najeriya Tinubu Ya Amince Na Tura Jakadu Labarai
  • Shugaba Tinubu Yakarawa Mambobin ASUU Kashi 40 Na Albashi Najeriya
  • Harkar Zirga Zirgar Jiragen Sama Ya Bunkasa A Kenya Afrika
  • Rundunar Tsaro Suna Cigaba Da Nasara Akan ‘Yan Ta’adda Tsaro
  • Mali Da Burkina Faso Za Su Haramta Wa Amurkawa Izinin Shiga Ƙasashen Su Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • CAF, Zata Ci Tarar Wasu Kasashe AFCON 2025 Wasanni
  • Jagoran Kasar Iran Yace Basa Bukatar Tallafin Kasar Amurka Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.