Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Rundunar Tsaro Suna Cigaba Da Nasara Akan ‘Yan Ta’adda
Published: December 11, 2025 at 1:29 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Rundunar Sojojin Najeriya ta yi gagarumar nasara a kan tawagar Bello Turji bayan ta halaka babban kwamandan ’yan bindiga, Kachalla Kallamu, a wani samame da ta kai a Sabon Birni, dake Jihar Sokoto.

Majiyar tsaro ta tabbatar da cewa dakarun Runduna ta 8 tare da haɗin gwiwar ‘yan sakai sun gudanar da aikin ne a safiyar ranar Litinin a kauyen Kurawa, inda suka kuma kashe wani babban mai kai wa Turji kayayyakin aiki.

Kallamu, ɗan asalin Garin Idi a Sabon Birni, ya dade yana addabar yankin da hare hare, garkuwa da mutane da kuma harin gonaki sannan ya koma yankin bayan ya tsere daga wani samamen soji a Yuni 2025.

Masani kan tsaro, Prof. Murtala Ahmed Rufa’i, ya bayyana Kallamu a matsayin Buzu (Tuareg) wanda iyayensa suka shigo daga Nijar cikin 1972, yana jagorantar kusan mutane 100, da ke aikata ta’addanci a Isa, Sabon Birni, Shinkafi, Goronyo, har ma da wasu yankuna na Zamfara da Nijar.

Dogon Zango shi ne yankin da ya fi karfi, inda yake tsara hare-hare kan kauyuka da dama sannan ya kuma kasance cikin wadanda suka kai mummunan harin watan Disamba 2021, lokacin da aka ƙona matafiya bisa umarnin Turji.

Rufa’i ya ce mutuwarsa da ta mataimakinsa Halliru ta haifar da rikicewa a cikin tsarin Turji, yana mai cewa yanzu ne lokacin da sojoji za su iya cakuɗa sansanin Dogon Zango kafin su nada sabon shugaba.

Sai dai ya yi gargadin cewa ba lallai rasuwar Kallamu ta yi tasiri sosai a kan manyan ayyukan Turji ba, domin bai kasance cikin sahun manyan kwamandojinsa ba.

Tsaro

Post navigation

Previous Post: Tsohon Minista Ngige Ya Shiga Komar EFCC
Next Post: Kanal Sani: Idan ‘Yan-Ta’adda Zasu Mutunta Sulhu To Gwamnati Ta Duba Hakan

Karin Labarai Masu Alaka

Yaki Ta Sararin Samaniya Ya Cigaba Tsakanin Amurka, Isra’ila Da Iran Afrika
Koriya Ta Arewa Ya Goyi Bayan Iran Wajen Zaben Sabon Jagora Mojtaba Khameni Afrika
An Tsinci Gawar Yarinya A Gombe Najeriya
Ministocin Kasar Asia Zasu Gudanar Da Taro A Kasar Malaysia Tsaro
Zanga-Zangar Adawa Da Harin Amurka Da Isra’ila Ya Zamo Tarzoma A Pakistani Afrika
Gwamnatin Kebbi Ta Samu Tankokin Yaki Tsaro

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jami’ai Daga Amurka Sunce Yakin Amurka Da Iran Zaizo Karshe
  • An Gudanar da Taron Kwana Biyu kan Tsarin Sa Ido da Tantance Ayyukan AGILE a Jihar Gombe 
  • Rwanda Zata Janye Dakaru Daga Mozambique
  • Ruwan Sama Yayi Ajalin Mutane 70 A Nairobi
  • Shugaban Amurka Yayi Watsi Da Tattaunawar Kawo Karshen Yaki Da Iran

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Kasar Ukraine Tayi Watsi Da Shiga Kungiyar NATO Labarai
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mataimakin Shugaban Kasa Ya Sauka A Jihar Kwara Labarai
  • ‘Yan Bindiga Sun Hallaka Mutane A Wajen Hakar Ma’adanai Dake Jihar Filato Najeriya
  • Jami’ai A Mexico Sun Tabbatar Da Kashe Shugaban Masu Shan Ƙwaya Nemesio Oseguera Labarai
  • Oliseh, Ya Ba Eric Chelle, Shawara Da Ya Zamo Mai Tsauri AFCON 2025. Wasanni
  • Hukumar Zabe A Najeriya Ta Cigaba Da Rijistar Katin Zabe Labarai
  • Gwamnatin Gombe Ta Dauki Sabbin Matakan Tsaro Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.