Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u Afrika
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa Afrika
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa Afrika
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed Afrika

Rundunar Tsaro Suna Cigaba Da Nasara Akan ‘Yan Ta’adda
Published: December 11, 2025 at 1:29 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Rundunar Sojojin Najeriya ta yi gagarumar nasara a kan tawagar Bello Turji bayan ta halaka babban kwamandan ’yan bindiga, Kachalla Kallamu, a wani samame da ta kai a Sabon Birni, dake Jihar Sokoto.

Majiyar tsaro ta tabbatar da cewa dakarun Runduna ta 8 tare da haɗin gwiwar ‘yan sakai sun gudanar da aikin ne a safiyar ranar Litinin a kauyen Kurawa, inda suka kuma kashe wani babban mai kai wa Turji kayayyakin aiki.

Kallamu, ɗan asalin Garin Idi a Sabon Birni, ya dade yana addabar yankin da hare hare, garkuwa da mutane da kuma harin gonaki sannan ya koma yankin bayan ya tsere daga wani samamen soji a Yuni 2025.

Masani kan tsaro, Prof. Murtala Ahmed Rufa’i, ya bayyana Kallamu a matsayin Buzu (Tuareg) wanda iyayensa suka shigo daga Nijar cikin 1972, yana jagorantar kusan mutane 100, da ke aikata ta’addanci a Isa, Sabon Birni, Shinkafi, Goronyo, har ma da wasu yankuna na Zamfara da Nijar.

Dogon Zango shi ne yankin da ya fi karfi, inda yake tsara hare-hare kan kauyuka da dama sannan ya kuma kasance cikin wadanda suka kai mummunan harin watan Disamba 2021, lokacin da aka ƙona matafiya bisa umarnin Turji.

Rufa’i ya ce mutuwarsa da ta mataimakinsa Halliru ta haifar da rikicewa a cikin tsarin Turji, yana mai cewa yanzu ne lokacin da sojoji za su iya cakuɗa sansanin Dogon Zango kafin su nada sabon shugaba.

Sai dai ya yi gargadin cewa ba lallai rasuwar Kallamu ta yi tasiri sosai a kan manyan ayyukan Turji ba, domin bai kasance cikin sahun manyan kwamandojinsa ba.

Tsaro

Post navigation

Previous Post: Tsohon Minista Ngige Ya Shiga Komar EFCC
Next Post: Kanal Sani: Idan ‘Yan-Ta’adda Zasu Mutunta Sulhu To Gwamnati Ta Duba Hakan

Karin Labarai Masu Alaka

Kasashen Amurka,Israela Da Iran Sun Amince Da Dakatar Da Yaki Afrika
Gwamnatin Najeriya Ta Tallafa Wa ’Yan Sanda Da Motoci Afrika
Tarayyar Turai Zasu Kirkiro Sojojin Haɗin Gwiwa Labarai
Isra’ila Ta Zantar Da Hukuncin Kisa Ga Masu Kai Hare Hare Labarai
Kasashen Yankin Gulf Sun Bukaci Amurka Takawo Karshen Iran Afrika
Kasar Chadi Ta Rufe Iyakar Ta Da Kasar Sudan Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Babu Alamar Tsagaita Wuta A Yakin Gabas Ta Tsakiya Afrika
  • Masu Ruwa da Tsaki akan Lamurran Siyasa sun Fara Maida Martani akan Matakin da Ministan Labaran Nigeria da wayar da kan Jama,a Idris Malagi na korar Daya Daga cikin Ma,aikatansa Saboda dalilai na Siyasa. da tsakiayar ranar Wannan larabace dai Mataimakin na Musamman akan yada Labarai ga Minista Malagi Malam Rani,u Ibrahim ya fitar da Wata sanarwar cewa Ministan ya Dakatar da Daya Daga cikin Ma,aikatansa Mai Suna Sa,idu Enagi Saboda ya fitar da Wani bayani a Kafar yada Labarai na sada zumunta dake Nuna Ministan ya shirya tsaf Domin takarar Gwamnan Jihar Neja a 2027. Malam Sa,idu Etsu Tsohon Dantakarar Shugaban cin Jam,iyyar APC a Nigeria Yace Matakin da Ministan ya Dauka yayi Dai dai Domin yanzu lokaci baiyi ba..ceu.. Shima Dattijon Siyasa a Jihar Neja Alh.Awaisu Giwa Kuta Yace Matakin da Ministan Labaran ya Dauka yayi Dai dai Domin yanzu Jihar Neja zaman Makoki Ake na fotinar Yan ta,adda ba wai Batun Neman Mukamin Siyasa ba..ceu .in.. To Sai jigon Jam,iyyar PDP Mai Adawa a Nigeria Hon.Yahaya Ability Yace Akwai kuskure Babba da Ministan ya tabka a dai dai Wannan Zamani na Siyasa duk da cewa Jihar Nejan na cikin Yanayi na masifar Yanbindiga..ceu..in .. Azaben Shekara ta 2023 Malagi ya kara yayi Takara Gwamnan Jihar Neja a jam,iyyar APC inda Gwamna Umar Bago ya kadashi a zaben fidda Gwani.
    Martanin Wasu ‘Yan Najeriya Ga Ministan Labarai Bisa Korar Dadiminsa Najeriya
  • Tattaunawar Nukiliya Tsakanin Iran Da Amurka Yana Tasirin Akan Farashin Albarkatun Mai Amurka
  • Rwanda Tana Keta Yarjejeniyar Zaman Lafiya – Tshisekedi Labarai
  • Babu Alamar Tsagaita Wuta A Yaki Da Akeyi Tsakanin Isra’ila Da Amurka Afrika
  • Jirgin Sojin Saman Najeriya Yayi Hatsari a Jihar Neja Labarai
  • Shugaba Tinubu Ya Umurci Janyewa Manyan Mutane ‘Yan Sanda Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Shugaba Trump Ya Yabawa Iran Bisa Bude Mashigar Hormuz Amurka
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.