Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

Rundunar Tsaro Suna Cigaba Da Nasara Akan ‘Yan Ta’adda
Published: December 11, 2025 at 1:29 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Rundunar Sojojin Najeriya ta yi gagarumar nasara a kan tawagar Bello Turji bayan ta halaka babban kwamandan ’yan bindiga, Kachalla Kallamu, a wani samame da ta kai a Sabon Birni, dake Jihar Sokoto.

Majiyar tsaro ta tabbatar da cewa dakarun Runduna ta 8 tare da haɗin gwiwar ‘yan sakai sun gudanar da aikin ne a safiyar ranar Litinin a kauyen Kurawa, inda suka kuma kashe wani babban mai kai wa Turji kayayyakin aiki.

Kallamu, ɗan asalin Garin Idi a Sabon Birni, ya dade yana addabar yankin da hare hare, garkuwa da mutane da kuma harin gonaki sannan ya koma yankin bayan ya tsere daga wani samamen soji a Yuni 2025.

Masani kan tsaro, Prof. Murtala Ahmed Rufa’i, ya bayyana Kallamu a matsayin Buzu (Tuareg) wanda iyayensa suka shigo daga Nijar cikin 1972, yana jagorantar kusan mutane 100, da ke aikata ta’addanci a Isa, Sabon Birni, Shinkafi, Goronyo, har ma da wasu yankuna na Zamfara da Nijar.

Dogon Zango shi ne yankin da ya fi karfi, inda yake tsara hare-hare kan kauyuka da dama sannan ya kuma kasance cikin wadanda suka kai mummunan harin watan Disamba 2021, lokacin da aka ƙona matafiya bisa umarnin Turji.

Rufa’i ya ce mutuwarsa da ta mataimakinsa Halliru ta haifar da rikicewa a cikin tsarin Turji, yana mai cewa yanzu ne lokacin da sojoji za su iya cakuɗa sansanin Dogon Zango kafin su nada sabon shugaba.

Sai dai ya yi gargadin cewa ba lallai rasuwar Kallamu ta yi tasiri sosai a kan manyan ayyukan Turji ba, domin bai kasance cikin sahun manyan kwamandojinsa ba.

Tsaro

Post navigation

Previous Post: Tsohon Minista Ngige Ya Shiga Komar EFCC
Next Post: Kanal Sani: Idan ‘Yan-Ta’adda Zasu Mutunta Sulhu To Gwamnati Ta Duba Hakan

Karin Labarai Masu Alaka

Pakistan Zata Karbi Tattaunawar Rikicin Gabas Ta Tsakiya Afrika
Shugaban Amurka Yace Zasu Kakabawa Mashigar Hormuz Takunkumi Afrika
Rundunar ‘Yan Sandan Kebbi Ta Dakile Yunkurin Garkuwa Da Mutune, Ta Kama Masu Laifi Afrika
Shugaba Tinubu Ya Gana Da Takwaransa Na Kasar Jamus Akan Sha’anin Tsaro Labarai
Shugaban Amurka Yace Zayyi Wahala A Cimma Yarjejeniya Tsakanin Isra’ila, Amurka Da Iran Amurka
Wasu Mayakan ‘Yan Tawaye Sunkai Hari Filin Jirgin Saman Kasar Kwango Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • ‘Yan Sanda A Gombe Sun Jaddada Shirin Yaƙi Da Munanan Dabi’u Afrika
  • An Gargadi Kasar Canada Game Da Tura Sojoji Lebanon Afrika
  • Pakistan Da Afghanistan Sun Shiga Kwana Na Biyar Suna Fafatawa Afrika
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari Afrika
  • Kyautata Dangantaka Tsakanin Jami’an Tsaro Da Al’umma Ce Mafita Najeriya
  • Amurka Ta Kwace Jirgin Mai Mallakar Rasha Amurka
  • Amurka Ta Kai ‘Yan Cirani Kamaru Afrika
  • Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf Ya Gana Da Shugaba Tinubu Siyasa
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.