Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama Afrika
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara Afrika
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe Afrika
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro Afrika
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa Afrika

Shugaba Tinubu Ya Umurci Janyewa Manyan Mutane ‘Yan Sanda
Published: November 24, 2025 at 3:36 AM | By: Nasiru Adamu Elhikaya | Updated: November 24, 2025

Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya ba da umurnin janye jami’an ‘yan sanda masu tsaron lafiyar manyan mutane ko wasu kusoshi na gwamnati.

A taro na musamman da babban sufeton ‘yan sanda IGP Kayode Egbetokun, manyan hafsoshin soja da daraktan jami’an tsaron farin kaya DSS, shugaban ya ce duk mai bukatar jami’ai masu damara don kare lafiyarsa sai ya rubuta bukata ga hukumar jami’an tsaron farar hula SIBIL DIFENS don samun masu kariyar.

Taron da ya gudana a fadar Aso Rock na da zummar samarda mafita ga kalubalen tsaro da kuma ceto matan makaranta da a ka sace a jihar Kebbi.

Shugaba Tinubu ya nuna damuwar yanda a ke samun karancin jami’an ‘yan sanda a yankunan karkara don tura dimbin jami’an ga manyan mutane da hakan ke haddasa karancinsu a aiyukan da ya dace su fi maida hankali a kai.

Sanarwa daga kakakin shugaban Bayo Onanuga ta ce shugaban ya ba da umurnin daukar sabbin jami’an ‘yan sanda 30,000 don kara yawan jami’an da yawansu bai kai bukatar da a ke da ita a samarda tsaro ba.

 

Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Post navigation

Previous Post: Ga Fili Ga Doki
Next Post: Malami: Gwamnatin APC Ta Gaza – “Yan-Kasa Kuwa Na Da Katin Zabe”

Karin Labarai Masu Alaka

Sarakunan Gombe Da Zazzau Sun Yi Kira Ga ‘Yan Najeriya Su Rungumi Haɗin Kai Da Zaman Lafiya Afrika
Shugaba Tinubu Ya Kafa Kwamitin Gaggawa Akan Cutar Ebola Afrika
Ferfesa Pantami Yasamu Tikitin Takarar Gwamnan Gombe A Jami’yar PDP Afrika
Hawan Gidan Gwamnati A Jihar Gombe Afrika
Ana Kokarin Kawo Karshen Matsalar Kashe Matafiya A Filato Afrika
NAHCON Ta Yaba da Nasarar Hajjin 2026, Ta Fara Shirin Hajjin Shekara Mai Zuwa Amurka

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Samar Da Tsaro A Jihar Kano Ba Sai An Sa Siyasa Ba! Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Sanda A Gombe Sun Jaddada Shirin Yaƙi Da Munanan Dabi’u Afrika
  • Sabunta Manhajar Ilimi A Duk Matakai Nasara Ce! Najeriya
  • Harin Bom Din Maiduguri Ya Kashe Mutane Biyar Ya Raunata Fiye Da Talatin Najeriya
  • Gaza Ga Albarusai Ga Yunwa Tsaro
  • Shugaba Trump Ya Jinjinawa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya Afrika
  • Tinubu Ya Aika Manyan Hafsoshin Tsaro Borno Afrika
  • Masar Ta Jibge Jiragen Yaki Marasa Matuka Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.