Shugabannin kungiyar Miyetti Allah Kautal Hore a Shiyar Arewa maso Gabashin Najeriya sun yi kira ga mambobin kungiyar da su kasance masu bin doka da oda, tare da tabbatar da zaman lafiya da sauran al’umma.
Shugabannin sun yi wannan kiran ne yayin wani taro da suka gudanar a jihar Gombe, inda suka tattauna batutuwan da suka shafi harkokin kiwo, tsaro, zaman lafiya da kuma ci gaban makiyaya a yankin.

Da yake maraba da tawagar, shugaban kungiyar Miyetti Allah Kautal Hore na jihar Gombe, Alhaji Ardo Chindo Abubakar, ya bayyana jin dadinsa da yadda aka zabi jihar Gombe a matsayin wurin gudanar da taron.
Alhaji Ardo Chindo ya kuma yaba da irin kokarin da gwamnatin jihar Gombe ke yi wajen inganta harkokin kiwo da kuma samar da yanayi mai kyau ga makiyaya.
Ya ce gwamnatin jihar ta kafa wani kwamiti da zai duba hanyoyin bude hanyoyin shanu, wuraren kiwo da kuma samar da rijiyoyin ruwa domin rage matsalolin da ke tsakanin makiyaya da manoma.
Ya kara da cewa, gwamnatin jihar na kokarin samar da kasuwar shanu ta kasa da kasa a Gombe, wanda ya ce hakan zai taimaka wajen bunkasa harkokin kasuwancin dabbobi da habaka tattalin arzikin jihar.

A nasa jawabin, shugaban kungiyar na shiyyar Arewa maso Gabas, Alhaji Nasiru Liman Jalbu, ya gode wa shugabannin jihar Gombe da sauran al’ummar jihar bisa irin kyakkyawar tarbar da aka yi wa tawagar.
Haka kuma, shugaban kungiyar na jihar Borno, Alhaji Musa Maina Harande, ya yaba da yadda aka shirya taron, yana mai cewa tattaunawa tsakanin shugabannin makiyaya na da muhimmanci wajen warware matsalolin da ke addabar harkokin kiwo da zaman lafiya.
Daya daga cikin muhimman batutuwan da suka tattauna a yayin taron shi ne batun shugaban kungiyar na kasa, Alhaji Abdullahi Bello Bodejo, wanda shugabannin suka ce ya shafe sama da watanni uku a tsare.
Shugabannin kungiyar sun yi kira ga gwamnonin jihohi da sarakunan gargajiya da su shiga tsakani wajen ganin an saukaka masa tare da samar da hanyar da za a tabbatar da an sake shi.
Sun bayyana cewa Alhaji Abdullahi Bello Bodejo ya taka muhimmiyar rawa wajen kokarin samar da zaman lafiya, tare da cewa ya bayar da gudunmawa wajen tallafawa harkokin siyasa da kuma nasarar jam’iyyar APC da zaben Shugaba Bola Ahmed Tinubu.
Bayan kammala taron, tawagar ta kai ziyara ga Kwamishinan Ma’aikatar Raya Dabbobi ta Jihar Gombe, Alhaji Salihu Baba Alkali, a ofishinsa.
Da yake jawabi ga tawagar, Kwamishinan ya yaba da irin gudunmawar da kungiyar ke bayarwa wajen bunkasa harkar kiwo da kuma habaka tattalin arzikin kasa.
Alhaji Salihu Baba Alkali Katukan Nafada ya kuma tabbatar wa shugabannin kungiyar cewa zai sake jaddada kiran da suka yi na neman a saki shugaban kungiyar na kasa, Alhaji Abdullahi Bello Bodejo.
Taron ya kuma jaddada muhimmancin bin doka da oda, zaman lafiya da fahimtar juna tsakanin makiyaya, manoma da sauran al’ummomin yankin Arewa maso Gabas.


