Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Pasto Yohanna Buru Ya Jagoranci Kiristoci Wajen Bikin Mauludi Tare Da Musulmi A Kaduna Afrika
  • Maulidin 2026: IMC Ta Yi Kira Da Ƙarfafa Zaman Lafiya Da Haɗin Kai A Najeriya Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya Taya Sarkin Musulmi Murnar Cika Shekaru 70, Ya Yi Masa Addu’ar Ƙarin Lafiya Da Tsawon Rai Afrika
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika

Tinubu Ya Buƙaci Musulmi Su Riƙe Haƙuri, Tawali’u Da Tausayi
Published: August 25, 2026 at 1:30 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Shugaban Ƙasar Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya buƙaci Musulmi a faɗin Najeriya da su rungumi koyarwa da kyawawan halayen Annabi Muhammad (SAW), yayin da suke bikin Maulidin Annabi na shekarar 2026.

Shugaban ya yi wannan kira ne a cikin wata sanarwa da mai ba shi shawara na musamman kan yaɗa labarai da dabarun sadarwa, Bayo Onanuga, ya fitar ranar Talata.

Ya ce bikin Maulidi bai kamata ya tsaya kawai kan tunawa da ranar haihuwar Annabi Muhammad (SAW) ba, sai dai ya kasance wata dama ga Musulmi su yi nazari, addu’a tare da koyon darussa daga kyakkyawar rayuwar Annabin.

Shugaba Tinubu ya buƙaci Musulmi su riƙe koyarwar Annabin, musamman ibada, haƙuri, juriya, yafiya, tawali’u da sadaukar da kai ga taimakon al’umma.

Ya kuma yi kira ga malaman addini da su yi amfani da wannan lokaci wajen yi wa Najeriya addu’a tare da jan hankalin mabiyansu su aiwatar da darussan da suka koya daga rayuwar Annabi Muhammad (SAW) wajen ƙara kishin ƙasa.

Haka kuma, Shugaban ya buƙaci Musulmin da ke bikin Maulidi su tallafa wa mabukata da masu rauni, tare da nuna musu ƙauna da kulawa.

Shugaba Tinubu ya kuma yi kira da a ci gaba da yi wa ƙasar addu’a domin samun nasara a kan matsalar rashin tsaro da sauran ƙalubalen da ke addabar wasu sassan Najeriya.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Nishadi, Sauran Duniya, Siyasa

Post navigation

Previous Post: Ceferin Ya Ce Ba Zai Yi Takarar Shugabancin FIFA Ba
Next Post: Pasto Yohanna Buru Ya Jagoranci Kiristoci Wajen Bikin Mauludi Tare Da Musulmi A Kaduna

Karin Labarai Masu Alaka

Jirgin Ruwan ‘Yan Gudun Hijira Ya Nitse Kogi A Tunisiya Labarai
Iran Zata Mayarwa Amurka Martanin Harin Kharg Afrika
Amurka Ta Nuna Damuwa Kan Matsalar ‘Yan Gudun Hijira A Najeriya Najeriya
Aikin Layin Dogon Kasar Uganda Zai Hade Kasar Da Tanzania Da Kwango Kimiya
Kano: Gwamna Abba Kabir Yusuf Ya Amince da Garo A Matsayin Mataimakinsa Na 2027 Afrika
Yau Litinin Za’a Mika Daliban Ga Iyayen Su Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Pasto Yohanna Buru Ya Jagoranci Kiristoci Wajen Bikin Mauludi Tare Da Musulmi A Kaduna
  • Tinubu Ya Buƙaci Musulmi Su Riƙe Haƙuri, Tawali’u Da Tausayi
  • Ceferin Ya Ce Ba Zai Yi Takarar Shugabancin FIFA Ba
  • Maulidin 2026: IMC Ta Yi Kira Da Ƙarfafa Zaman Lafiya Da Haɗin Kai A Najeriya
  • Alejandro Balde Na Dab Da Komawa Manchester United Daga Barcelona

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Shirin Dare 26.11.2025 Rediyo
  • Kasar Saudiya Zatayi Gwajin Noman Dabino A Kano Labarai
  • Zamfara: Sai Mun Hada Kai Don Kawo Karshen Ta’addanci Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Akwai Bukatar Hukunci Mai Tsanani Ga Duk Wanda Yayi Fyade Najeriya
  • Hukumomin Tsaron Najeriya Ne Suka Bukaci Amurka Ta Turo Musu Sojoji Amurka
  • Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Zuwa Jami’ar Sheikh Dahiru Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Kasashen Turai: Bazamu Yarda Da Dokar Harajin Trump Ba Labarai
  • NUJ Gombe Ta Ƙarfafa Bin Ɗa’a A Aikin Jarida, Ta Kaddamar Da Kwamitin Ladabtarwa Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.