Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Tinubu Ya Buƙaci Musulmi Su Riƙe Haƙuri, Tawali’u Da Tausayi Afrika
  • Maulidin 2026: IMC Ta Yi Kira Da Ƙarfafa Zaman Lafiya Da Haɗin Kai A Najeriya Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya Taya Sarkin Musulmi Murnar Cika Shekaru 70, Ya Yi Masa Addu’ar Ƙarin Lafiya Da Tsawon Rai Afrika
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika

Pasto Yohanna Buru Ya Jagoranci Kiristoci Wajen Bikin Mauludi Tare Da Musulmi A Kaduna
Published: August 25, 2026 at 1:47 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Wani fitaccen malamin addinin Kirista daga jihar Kaduna, Fasto Dr. Yohanna Buru, wanda ya yi fice wajen inganta zaman lafiya da fahimtar juna tsakanin mabiya addinai, ya shiga cikin dubban Musulmi domin bikin Maulidin Annabi Muhammad (SAW) a jihar Kaduna.

Fasto Buru, wanda shi ne Babban Fasto na Christ Evangelical and Life Intervention Ministry, ya ce wannan shi ne karo na 11 a jere da yake halartar bukukuwan Mauludi tare da Musulmi a Kaduna da sauran sassan Arewacin Najeriya.

Faston ya halarci bikin ne tare da wasu shugabannin Kiristoci, ciki har da Fasto George John, Rabaran Rawland Sanda da Gabriel Stephen, inda suka shiga cikin dubban Musulmi da suka taru a filin Murtala Mohammed Square da ke Kaduna domin tunawa da haihuwar Annabi Muhammad (SAW).

Da yake jawabi a wajen taron, Fasto Buru ya ce halartar Mauludi da yake yi na daga cikin kokarinsa na inganta zaman lafiya, hakuri da juna, mutunta addinai da kuma karfafa kyakkyawar alaka tsakanin Kiristoci da Musulmi.

Ya ce bukukuwan Mauludi na samar da wata dama ta musamman da mabiya addinai daban-daban za su hadu, su tattauna tare da kara fahimtar juna, yana mai cewa zaman lafiya na bukatar tattaunawa, hakuri da kuma mutunta juna.

A cikin wata lacca kan zaman lafiya da hadin kai, Fasto Buru ya bayyana Annabi Muhammad (SAW) a matsayin Manzo wanda koyarwarsa kan zaman lafiya, soyayya da tausayi ta shafi daukacin bil’adama.

Ya ce, “Annabi Muhammad (SAW) Manzo ne ga dukkan bil’adama, ba tare da la’akari da kabila, al’ada, yanki, launi, jinsi ko kasa ba.”

Fasto Buru ya yi kira ga ‘yan Najeriya daga kabilu da addinai daban-daban da su rungumi juna, su yafe wa juna kura-kuran baya, sannan su hada kai wajen gina kasa mai zaman lafiya da hadin kai.

Ya ce Kiristoci da Musulmi sun yi imani da Ubangiji guda, don haka ya kamata su yi amfani da Littafi Mai Tsarki da Al-Qur’ani wajen samun jagoranci kan yadda za a tabbatar da zaman lafiya da fahimtar juna.

Faston ya kuma bayyana cewa halartar bukukuwan Mauludi da yake yi ba ya nufin ya yi watsi da addininsa na Kirista, yana mai cewa yin hakan wani bangare ne na kokarinsa na karfafa fahimtar juna tsakanin mabiya addinai.

Ya bayyana cewa a kowace shekara yana halartar bukukuwan Mauludi sama da 30 a jihohin Najeriya daban-daban da kuma wasu kasashen makwabta, domin yin murnar tare da Musulmi da kuma yada sakon zaman lafiya, hadin kai da hakurin addini.

Ya ce, “A kowace shekara ina halartar bukukuwan Mauludi sama da 30 daga jiha zuwa jiha, har ma da wasu kasashe makwabta, da nufin yin murnar tare da Musulmi da kuma inganta zaman lafiya, hadin kai da hakurin addini.”

Fasto Buru ya bukaci Kiristoci da Musulmi da su yi amfani da wannan lokaci na Mauludi wajen yada soyayya, yafiya, hadin kai da zaman lafiya a fadin Najeriya.

Shi ma da yake jawabi, Rabaran Rawland Sanda ya ce shugabannin Kiristoci na ci gaba da amsa gayyatar Musulmi domin halartar bukukuwan Mauludi, a matsayin wata hanya ta karfafa alaka da fahimtar juna tsakanin mabiya addinan biyu.

Ya ce, “A kowace shekara Musulmi kan gayyace mu zuwa bukukuwan Mauludi, kuma kullum muna zuwa domin yin murna tare da su, saboda mun yi imani da inganta zaman lafiya, hadin kai da kyakkyawar alaka tsakanin mutane masu addinai daban-daban.”

Ya kara da cewa Kiristoci ma suna gayyatar Musulmi zuwa majami’u a lokacin bikin Kirsimeti domin tunawa da haihuwar Yesu Almasihu.

Ya ce, “Muna taya Musulmi a fadin duniya murna, tare da addu’ar samun zaman lafiya da hadin kai a kasarmu.”

Shi ma wani malamin addinin Musulunci, Imam Mohammed Musa, tare da Imam Iliyasu Yusuf na Zariya, Kaduna, sun yabawa Fasto Buru da sauran shugabannin Kiristoci bisa halartar bikin Mauludi tare da Musulmi.

Malaman sun bayyana wannan al’ada a matsayin wata muhimmiyar hanya da ke karfafa fahimtar juna, mutunta juna da zaman lafiya tsakanin mabiya addinai daban-daban.

Sun ce tsawon shekaru 11, Fasto Dr. Yohanna Buru ya kasance yana halartar bukukuwan Mauludi tare da Musulmi a Kaduna da sauran sassan Arewacin Najeriya, lamarin da suka ce ya zama muhimmiyar hanya wajen hada kan mabiya addinai daban-daban.

Malaman sun kuma yi kira ga Gwamnatin Tarayya da ta yi la’akari da bai wa Fasto Buru lambar yabo ta kasa, bisa irin gudunmawar da yake bayarwa wajen inganta zaman lafiya, hakurin addini da fahimtar juna tsakanin mabiya addinai a Najeriya.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Nishadi, Sauran Duniya

Post navigation

Previous Post: Tinubu Ya Buƙaci Musulmi Su Riƙe Haƙuri, Tawali’u Da Tausayi

Karin Labarai Masu Alaka

Jami’an Tsaro Suna Farautar Wasu ‘Yan Ta’adda A Najeriya Afrika
Gobara Ta Tashi A Hukumar FIRS Dake Abuja Najeriya
Kasar Habasha Da Turkiyya Sun Kulla Yarjejeniyar Makamashi Afrika
Tashoshin Mai Basa Iya Loda Mai A Rasha Labarai
‘Yan Bindiga Sun Kashe Fiye Da Mutane 15 A Kasar Australiya Labarai
Zanga-Zangar Adawa Da Harin Amurka Da Isra’ila Ya Zamo Tarzoma A Pakistani Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Pasto Yohanna Buru Ya Jagoranci Kiristoci Wajen Bikin Mauludi Tare Da Musulmi A Kaduna
  • Tinubu Ya Buƙaci Musulmi Su Riƙe Haƙuri, Tawali’u Da Tausayi
  • Ceferin Ya Ce Ba Zai Yi Takarar Shugabancin FIFA Ba
  • Maulidin 2026: IMC Ta Yi Kira Da Ƙarfafa Zaman Lafiya Da Haɗin Kai A Najeriya
  • Alejandro Balde Na Dab Da Komawa Manchester United Daga Barcelona

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Amurka Zata Bawa Ukraine Tsaro Na Musamman Amurka
  • Kamfanin Mai Mallakar Saudiya Aramco Zai Sanja Hanyar Fitar Da Danyen Mai Labarai
  • Iran Zata Kai Hari Tashar Makamashin Ruwa A Gulf Afrika
  • Tsohon Minista Ngige Ya Shiga Komar EFCC Najeriya
  • Maulidin 2026: IMC Ta Yi Kira Da Ƙarfafa Zaman Lafiya Da Haɗin Kai A Najeriya Afrika
  • Sakataren Tsaron Amurka Yace Baza’a Bayyana Bidiyon Kai Hari Akan Jirgin Ruwa Ba Amurka
  • Lawal, Filin Wasa Na Rashidi Yekini Ko Turai Iyaka Wasanni
  • Gwamnan Jihar Zamfara Dauda Lawal Ya Bar PDP Ya Koma APC Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.