Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u Afrika
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa Afrika
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa Afrika
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed Afrika

Iran Zata Kai Hari Tashar Makamashin Ruwa A Gulf
Published: March 23, 2026 at 7:19 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

A jiya Lahadi Iran ta bayyana cewa za ta kai hari kan tashar makamashi da na ruwa na ƙasashen maƙwabta a yankin Gulf, a matsayin martani idan Shugaban Amurka, Donald Trump, ya aiwatar da barazanar da ya yi na kai hari kan tashar wutar lantarki na Iran cikin sa’o’i 48, lamarin da ke ƙara tsananta rikicin da ya shafe makonni uku yana gudana.

Hasashen irin waɗannan hare-hare na ramuwar gayya kan kayayyakin more rayuwa na fararen hula na iya ƙara tsananta rikicin yankin, tare da girgiza kasuwannin duniya lokacin da za su sake buɗewa a safiyar Litinin.

An ji ƙararrawar gargadin hare-haren sama a sassan Isra’ila tun daga farkon safiyar Lahadi, domin sanar da zuwan makamai masu linzami daga Iran, bayan da mutane da dama suka jikkata a daren jiya sakamakon hare-hare biyu daban-daban a garuruwan Arad da Dimona da ke kudancin Isra’ila.

Sojojin Isra’ila sun ce bayan wasu sa’o’i sun fara kai hare-hare kan Tehran a matsayin martani.

Trump ya yi barazanar a daren jiya cewa zai “lalata gaba ɗaya” tashoshin samar da wutar lantarki na Iran idan Tehran ba ta buɗe mashigin ruwan Hormuz gaba ɗaya cikin sa’o’i 48 ba. Wannan na zuwa ne kusan kwana guda bayan ya yi magana kan “rage zafin yaƙin.” Ya kuma yi wannan sabuwar barazana ne a daidai lokacin da dakarun ruwan Amurka da manyan jirage masu sauka cikin ruwa ke kan hanyarsu zuwa yankin.

Afrika, Amurka, Labarai, Sauran Duniya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Sarkin Gombe Ya Ziyarci Gwamna Inuwa Yahaya
Next Post: An Zargi Babban Mai Gabatar Da Kara A Kotun Duniya Ta ICC

Karin Labarai Masu Alaka

Iran Ta Kama Wasu ‘Yan Leken Asiri Afrika
Makiyaya Sun Shiga Matsala Sakamakon Fari A Kasar Kenya Afrika
Jirgin Hakar Mai Daga Turkiyya Ya Isa Mugadishu Afrika
Nigeria Zata Bude Asusun Dala Bilyan Biyu Don Habaka Sashin Makamashi Labarai
Dubban ‘Yan Gudun Hijira Sun Halaka Amurka
Babban Hafsan Tsaron Najeriya Ya Gargadi Masu Tayar Da Hankali Najeriya

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Sojin Saman Najeriya Sunyi Gagarumar Nasara A Yankin Borno Najeriya
  • Ghana Ta Haramta Hakar Ma’adinai A Gandunan Dajin Data Kebe, Labarai
  • Taron Sulhu Tsakanin Addinai Mabanbanta Na Arewacin Najeriya Labarai
  • ‘Yan Tada Kayar Baya Sun Tayar Da Bom A Maiduguri Labarai
  • Shugaba Trump Ya Bukaci A Cigaba Da Zanga Zanga A Iran Labarai
  • Tinubu Ya Nuna Alhinin Rasuwar Janar Rabe Abubakar, Ya Jajanta wa Iyalansa Afrika
  • Sojoji Sunkai Farmaki Gidan Dan Adawa A Kasar Uganda Bobi Wine Afrika
  • Rundunan  ‘Yan Sandan Jihar Bauchi, Ta Miƙa Miyagun Ƙwayoyi Da Ta Kama Wa NDLEA. Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.