Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro Labarai
  • Za A Cigaba Da Tattaunawa Domin Kawo Karshen Yakin Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Iran Ta Kama Wasu ‘Yan Leken Asiri
Published: March 11, 2026 at 8:48 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Ahalinda ake ciki kuma, Iran ta kama mutane da dama ciki har da wani dan kasar ketare kan zargin suna yi wa “makiyan” kasar leken asiri, kamar yadda ma’aikatar tsaron kasar ta fada ranar talata, a dai dai lokacin da ake ci gaba da yakin hadin guiwar da Amurka da Isra’ila suka kaddamar kan kasar.

Ba tare da ta ambaci kasar da wadanda aka kaman suka fito ba, ma’aikatar tsaron Iran tace dan kasar ketaren “yana yi wa Amurka da Isra’ila leken asiri, kuma dan koren wasu kasashe biyu da suke yankin Gulf, kamar yadda wata kafar yada labaran kasar ta fada.

A shekarun baya bayan nan, rundunar juyin juya hali ta Iran ta kama gomman mutane wadanda asalin su ‘yan Iran ne masu ruwa biyu, kan zargin leken asiri da kuma harkar tsaro.

A ranar 28 ga watan Febwairu ne Amurka da Isra’ila suka kaddamar hare hare kan Iran har suka kashe shugaban addinin kasar Ayatollah Ali Khameni, da wasu kwamandajin kasar.

Afrika, Amurka, Labarai, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Hukumar Zabe Ta Saukaka Gudanar Da Rijistar Katin Zabe A Najeriya
Next Post: Ukraine Ta Tura Tawagar Kwarerru Zuwa Kasashen Larabawan Domin Basu Kariya

Karin Labarai Masu Alaka

Tinubu, Akpabio da Ministoci 9 Zasu Tafi Ƙasar Birtaniya Afrika
An Saka Dokar Hana Fita A Jos Ta Arewa Afrika
Shugaba Trump Ya Yabawa Iran Bisa Bude Mashigar Hormuz Amurka
Sakataren Harkokin Wajen Amurka Yace Rahoton Kasashe Biyar Akan Rasha Yana Dauke Da Damuwa Amurka
Sabon Magajin Garin New York Zai Soke Wasu Dokoki Amurka
Jirgin Sama Mai Saukar Ungulu Ya Kashe Mutane Biyar A Tanzaniya Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Shugaba Trump Ya Yabawa Iran Bisa Bude Mashigar Hormuz
  • Shugaba Tinubu Yasa Hannu Kan Dokar Kasafin 2026
  • Shugaba Tinubu Yace Bazai Bawa ‘Yan Najeriya Kunya Ba
  • Jami’an Askarawa A Zamfara Sun Kama Na’urorin Fashewa Da Makudan Kuɗaɗe
  • Jami’yar ADC A Najeriya Ta Kori Nafiu Bala

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Majalisar Dottijan Najeriya Ta Amince Da Tura Sakamakon Zabe Ta Na’ura Labarai
  • Amurka Na Zargi Kasar Rwanda Da Kokarin Saba Yarjejeniyar Zaman Lafiya Amurka
  • Kasar Afirka Ta Kudu Ta Tsare Wasu Amurkawa Amurka
  • Prime Ministan Pakistan Yace Zai Karbi Bakoncin Tattaunawar Amurka Da Iran Afrika
  • Shugaban Ƙasar China Zai Karbi Bakwancin Shugaban Koriya Ta Kudu Afrika
  • Amurka Da Iran Sun Tattauna A Kasar Pakistan Afrika
  • Mutane 27 Sun Rasa Rayukan Su A Najeriya Afrika
  • Kasar Amurka Da Rasha Zasu Kawo Karshen Tsagaita Nukiliya Amurka
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.