Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Kyautata Dangantaka Tsakanin Jami’an Tsaro Da Al’umma Ce Mafita
Published: November 22, 2025 at 3:30 AM | By: Yusuf Aliyu Harande | Updated: November 23, 2025

Masana harkokin tsaro a Najeriya sun bayyana cewa kyakkyawar alaka da fahinta tsakanin jami’an tsaro da al’umma, suna da gagarumin tasiri wajen magance matsalolin tsaro da samun zaman lafiya mai dorewa.
A wata tattaunawa ta musamman da sashen hulda tsakanin farar hula da jami’an soji da shelkwatar rundunar ta shirya da manema labarai a Jos, jihar Filato, masana harkokin tsaro, jami’an soji da ‘yan jarida sun dauki wuni guda suna fadakar da juna matakan da kowa zai bi wajen samadda masalaha kan matsalolin tsaro da suka addabi Najeriya.
Birgediya Janar Sani Usman Kukasheka mai ritaya, wanda ya gabatar da kasida mai taken “Tasirin Fasahar dake tasowa kan kafafen watsa labarai da hadin gwiwa tsakanin soji da kafafen watsa labarai”, ya bayyana cewa idan har ‘yan jarida sun fahinci yadda soja ke gudanar da aikinsu, suka kuma fadakar da al’umma, ba shakka za’a sami ci gaba.
Madam Ayuku Pwaspo, shugabar kungiyar ‘yan Jarida ta kasa reshen jihar Filato, ta bukaci manema labarai su gudanar da aikinsu bisa ka’ida don hadin kan kasa.
Shugaban sashen hulda tsakanin farar hula da soji, Manjo Janar Musa Etsu-Ndagi yace ‘yan jarida na da gagarumin gudunmawar fadakar da jama’a yadda soja ke aiki.
Hajiya Hadiza Hassan, ‘yar jarida dake aiki a gidan Rediyo da Talabijin na Unity a Jos, tace ta karu sosai daga tattaunawar.
Wassu faifan bidiyo da hotuna da rundunar sojin da nuna sun bayyana irin tallafi da sojoji ke baiwa al’umma da suka hada da gyara da gina makarantu da asibitoci, tallafin kayan abinci ga wadanda suka shiga ibtila’i da sauransu.
Najeriya

Post navigation

Previous Post: Manya-Manyan Wasannin Wannan Makon
Next Post: Tsananta Hukunci Ga Masu Fyade Kan Takaita Cin Zarafin Yara

Karin Labarai Masu Alaka

An Kama Tsohon Jakadan Birtaniya A Amurka Peter Mandelson Amurka
‘Yan Ta’adda Sun Kashe Sojoji A Kauyen Wanka Jihar Filato Afrika
Tsohuwar Ministan Albarkatun Mai Ta Bayyana A Kotu Najeriya
Mabiya Addinin Kirista Da ‘Yan Bindiga Suka Sace Sun Kubuta Labarai
Sojojin Najeriya Sun Kwato Mutane Daga Hannun Masu Garkuwa Najeriya
Samar Da Tsaro A Jihar Kano Ba Sai An Sa Siyasa Ba! Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Kungiyar Gwamnonin Arewacin Najeriya Tayi Kakkausar Lafazi Game Da Harin Maiduguri
  • Tinubu, Akpabio da Ministoci 9 Zasu Tafi Ƙasar Birtaniya
  • Tinubu Ya Aika Manyan Hafsoshin Tsaro Borno
  • Lauyoyi Sun Gurfanar Da Wani A Kotu Bisa Fasa Korin Kiyashi A Kenya
  • Anfara Gangamin Kafa Dokoki Masu Tsanani Ga ‘Yan Luwadi A Senegal

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • ‘Yan Bindiga Sun Kama Akalla Mutane 13 A Wani Coci A Jihar Kogi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Majalisar Wakilai Ta Rikon Kwaryar Nijar Ta Gudanar Da Zama Karo Na Biyu Afrika
  • Matsalolin Masarautun Kano Sun Kawo Karshe Najeriya
  • Farashin Danyen Mai Ya Tashi A Kasuwannin Duniya Afrika
  • Alhassan Yayi Nasarar Kifar Da Wurkilili A Gasar Damben Gargajiya Wasanni
  • Shugaba Tinubu Ya Rantsar Da Christ Musa Ministan Tsaro Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Kasar Iceland Ta Kauracewa Bikin Gasar Wakokin Shekara Mai Zuwa Labarai
  • Mayakan M23 Sun Tsagaita Wuta A Gabashin Kwango Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.