Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • PDP Ta Tsayar da Goodluck Jonathan Takarar Shugaban Kasa Afrika
  • Hawan Gidan Gwamnati A Jihar Gombe Afrika
  • Hawan Babbar Sallah A Masarautar Kaltungo Dake Jihar Gombe Afrika
  • Sarkin Gombe Ya Yabi Nasarorin Inuwa Yahaya A Fannonin Tsaro Da Raya Kasa Afrika
  • Tinubu Ya Jaddada Aniyar Rage Tsadar Rayuwa Da Samar da Ayyukan Yi Afrika

Kyautata Dangantaka Tsakanin Jami’an Tsaro Da Al’umma Ce Mafita
Published: November 22, 2025 at 3:30 AM | By: Yusuf Aliyu Harande | Updated: November 23, 2025

Masana harkokin tsaro a Najeriya sun bayyana cewa kyakkyawar alaka da fahinta tsakanin jami’an tsaro da al’umma, suna da gagarumin tasiri wajen magance matsalolin tsaro da samun zaman lafiya mai dorewa.
A wata tattaunawa ta musamman da sashen hulda tsakanin farar hula da jami’an soji da shelkwatar rundunar ta shirya da manema labarai a Jos, jihar Filato, masana harkokin tsaro, jami’an soji da ‘yan jarida sun dauki wuni guda suna fadakar da juna matakan da kowa zai bi wajen samadda masalaha kan matsalolin tsaro da suka addabi Najeriya.
Birgediya Janar Sani Usman Kukasheka mai ritaya, wanda ya gabatar da kasida mai taken “Tasirin Fasahar dake tasowa kan kafafen watsa labarai da hadin gwiwa tsakanin soji da kafafen watsa labarai”, ya bayyana cewa idan har ‘yan jarida sun fahinci yadda soja ke gudanar da aikinsu, suka kuma fadakar da al’umma, ba shakka za’a sami ci gaba.
Madam Ayuku Pwaspo, shugabar kungiyar ‘yan Jarida ta kasa reshen jihar Filato, ta bukaci manema labarai su gudanar da aikinsu bisa ka’ida don hadin kan kasa.
Shugaban sashen hulda tsakanin farar hula da soji, Manjo Janar Musa Etsu-Ndagi yace ‘yan jarida na da gagarumin gudunmawar fadakar da jama’a yadda soja ke aiki.
Hajiya Hadiza Hassan, ‘yar jarida dake aiki a gidan Rediyo da Talabijin na Unity a Jos, tace ta karu sosai daga tattaunawar.
Wassu faifan bidiyo da hotuna da rundunar sojin da nuna sun bayyana irin tallafi da sojoji ke baiwa al’umma da suka hada da gyara da gina makarantu da asibitoci, tallafin kayan abinci ga wadanda suka shiga ibtila’i da sauransu.
Najeriya

Post navigation

Previous Post: Manya-Manyan Wasannin Wannan Makon
Next Post: Tsananta Hukunci Ga Masu Fyade Kan Takaita Cin Zarafin Yara

Karin Labarai Masu Alaka

Take Hakkin Dan Adam Zai Haifar Da Juyin Juya Hali A Najeriya Najeriya
Shugaba Tinubu Yace Bazai Bawa ‘Yan Najeriya Kunya Ba Afrika
Jam’iyar APC A Jihar Gombe Ta Tsayar Da Jamilu Isiyaku Gwamna Takarar Gwamna Afrika
Shugaba Tinubu ya mika sunayen Sabbin Shugabannin NMDPRA da NUPRC Bayan Murabus Din Farouk Ahmad Da Gbenga Komolafe Najeriya
Hamma Saleh Ya Yi Fatali da Bai Wa Pantami Takarar Gwamna a PDP Afrika
Tinubu, Akpabio da Ministoci 9 Zasu Tafi Ƙasar Birtaniya Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • PDP Ta Tsayar da Goodluck Jonathan Takarar Shugaban Kasa
  • Hawan Gidan Gwamnati A Jihar Gombe
  • Hawan Babbar Sallah A Masarautar Kaltungo Dake Jihar Gombe
  • Sarkin Gombe Ya Yabi Nasarorin Inuwa Yahaya A Fannonin Tsaro Da Raya Kasa
  • Tinubu Ya Jaddada Aniyar Rage Tsadar Rayuwa Da Samar da Ayyukan Yi

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Kasashen Da Dama Na Neman Hanyar Cigaba Da Dakon Makamashi Afrika
  • Ana Cigaba Da Yaki Tsakanin Amurka Da Isra’ila Da Kasar Iran Afrika
  • An Gano Wani Kurkukun Sirri Da Ake Azaftar Da Mutane A Kasar Libya Afrika
  • Hukumar EFCC Ta Kwace Gidan Tsohon Antoni Janar Abubakar Malami Najeriya
  • Za’a Ninka Shekarun Zama A Gidan Kurkuku Ga Masu Auren Jinsi A Senegal Afrika
  • Jam’iyyar PDP Na Kara Tsunduma Cikin Mawuyacin Hali Shirye-Shirye
  • Ana Cigaba Da Jimamin Rasuwar Mataimakin Gwamnan Bayelsa Najeriya
  • Rundunar Sojin KTK Ta Harba Makami Teku Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.