Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai Afrika
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari Afrika
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe Afrika
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS Afrika
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe Afrika

Kasashen Daular Larabawa Tare Da Saudiya Da Jordan Sunyi Allah Wadai Da kasar Israel
Published: February 9, 2026 at 10:05 PM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: February 10, 2026

A ranar Litinin kasashen Saudi Arabia, Jordan da kasashen Haddadiyar Daular Larabawa sun yi Allah wadai da yunkurin da Isra’ila take yi na saukakawa ‘yan kasar ta yadda zasu samu matsuguni a yankunan yammacin kogin Jordan da ke mallakin Palastine.

Shawarar da majalisar tsaron Isra’ila ta yanke ranar Lahadi, zai saukakawa yahudawa wajen siyen filaye a yankin, kuma zai bawa Isra’ila karin karfin iko a guraren da a bisa zato suna karkashin ikon Palasdinawa ne, a cewar wasu manyan ministocin Isra’ila 2.

Daya daga cikin ministocin dake da ra’ayin tsananin kishin kasa, ministan kudi Bezalel Smotrich, da yake sanar da hukuncin, ya ce gwamnatin sa zata ci gaba da rushe ra’ayin wanzuwar kasar Palestine.

Wani jawabi daga ministocin kasashen gabas ta tsakiya da sauran kasahen larabawa, da suka hada da Masar da Turkiya sun yi Allah wadai da wannan kuduri, da ya karya dokokin kasa da kasa, kuma zai kawo kalubale ga mafitar da ake so a samu na kowanne bangare ya mallaki kasar sa, da kuma wanzuwar zaman lafiya a yankin.

Afrika, Labarai, Sauran Duniya

Post navigation

Previous Post: Ana Cigaba Da Samun Hare Hare Da Jiragen Marasa Matuki A Sudan
Next Post: Maikaba Ya Yi Murabus A Matsayinsa Kocin Wikki Tourist FC

Karin Labarai Masu Alaka

Ana Cigaba Da Samun Hare Hare Da Jiragen Marasa Matuki A Sudan Labarai
Sojojin Amurka Sun Kutsa Cikin Kasar Iran Labarai
Kasashen Yankin Gulf Sun Bada Sanarwa Afrika
Kudaden Shigan Kasar Namibia Ya Bunkasa Saboda Tashin Farashin Gwal Labarai
Kasar Aljeriya Ta Soke Yarjejeniyar Jirgin Sama Tsakaninta Da Daular Larabawa Labarai
Yaki Ta Sararin Samaniya Ya Cigaba Tsakanin Amurka, Isra’ila Da Iran Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Motar Kungiyar Kwallon Kafar Bayelsa United Ta Yi Hatsari Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Shugabannin Sojojin Najeriya sun Kai Ziyarar Aiki Maiduguri  Afrika
  • Maikaba Ya Yi Murabus A Matsayinsa Kocin Wikki Tourist FC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Hawan Nasarawa A Jihar Kano Afrika
  • Wasu Lauyoyi Sunyi Murabus Yayin Gudanar Da Wata Shari’a A Kasar Amurka Amurka
  • Majalisar Wakilai Ta Rikon Kwaryar Nijar Ta Gudanar Da Zama Karo Na Biyu Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Zata Farfado Da Cibiyar Koyon Sana’oi Ta Dangote Afrika
  • Rahoton MDD Yace An Kashe Fiye Da Farar 1000 A Sudan Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.