Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian ya bayyana cewa, kasar Iran na ganin daman samun sakamako mai kyau daga zagaye na uku na tattaunawa da Amurka, a ranar Laraba, yayin da wata tawaga ta tashi zuwa birnin Geneva domin tattaunawa kan shirin nukiliyar na Tehran.
Wani babban jami’in gwamnatin Amurka ya fada a ranar Litinin cewa manzon Amurka Steve Witkoff da surukin shugaban Amurka Donald Trump Jared Kushner na shirin ganawa da tawagar Iran karkashin jagorancin ministan harkokin wajen kasar Abbas Araqchi a Geneva ranar Alhamis.
A farkon wannan wata ne kasashen biyu suka koma tattaunawa kan shirin nukiliyar da aka dade ana takaddama a kai, a daidai lokacin da Amurka ke kara karfafa karfin soji a yankin gabas ta tsakiya, gabanin kai hare-hare kan Jamhuriyar Musulunci ta Iran. Iran ta yi barazanar kai hari kan sansanonin Amurka da ke yankin idan aka kai mata hari.
Trump a ranar 19 ga Fabrairu ya ce yana ba Tehran kusan kwanaki 10 zuwa 15 don yin yarjejeniya.


