Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • PDP Ta Tsayar da Goodluck Jonathan Takarar Shugaban Kasa Afrika
  • Hawan Gidan Gwamnati A Jihar Gombe Afrika
  • Hawan Babbar Sallah A Masarautar Kaltungo Dake Jihar Gombe Afrika
  • Sarkin Gombe Ya Yabi Nasarorin Inuwa Yahaya A Fannonin Tsaro Da Raya Kasa Afrika
  • Tinubu Ya Jaddada Aniyar Rage Tsadar Rayuwa Da Samar da Ayyukan Yi Afrika

Shugaban Kasar Iran Ya Bayyana Samun Sakamako Mai Kyau A Tattaunawa Da Amurka
Published: February 25, 2026 at 5:19 PM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: February 25, 2026

Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian ya bayyana cewa, kasar Iran na ganin daman samun sakamako mai kyau daga zagaye na uku na tattaunawa da Amurka, a ranar Laraba, yayin da wata tawaga ta tashi zuwa birnin Geneva domin tattaunawa kan shirin nukiliyar na Tehran.

Wani babban jami’in gwamnatin Amurka ya fada a ranar Litinin cewa manzon Amurka Steve Witkoff da surukin shugaban Amurka Donald Trump Jared Kushner na shirin ganawa da tawagar Iran karkashin jagorancin ministan harkokin wajen kasar Abbas Araqchi a Geneva ranar Alhamis.

A farkon wannan wata ne kasashen biyu suka koma tattaunawa kan shirin nukiliyar da aka dade ana takaddama a kai, a daidai lokacin da Amurka ke kara karfafa karfin soji a yankin gabas ta tsakiya, gabanin kai hare-hare kan Jamhuriyar Musulunci ta Iran. Iran ta yi barazanar kai hari kan sansanonin Amurka da ke yankin idan aka kai mata hari.

Trump a ranar 19 ga Fabrairu ya ce yana ba Tehran kusan kwanaki 10 zuwa 15 don yin yarjejeniya.

Amurka, Labarai, Sauran Duniya

Post navigation

Previous Post: Shugaba Trump Yace Bazai Bari Iran Ta Mallaki Nukiliya Ba
Next Post: Fafaroma Leo Zai Ziyarci Kasashen Afirka

Karin Labarai Masu Alaka

‘Yan Sanda A Tsibirin Bahamas Sun kama Mijin Wata Ba Amurkiya Amurka
Iran Zata Mayarwa Amurka Martani Amurka
Thailand Da Cambodia Sun Fara Tattauunawa Kan Batun Tsagaita Wuta Labarai
Ga Dukkan Alamu Yaki Tsakanin Rasha Da Ukraine Bai Kare Ba Sauran Duniya
Gwamnan Jihar Gombe Ya Umurci A Rufe Makarantu Labarai
Ministan Harkokin Wajen Iran Yagana Da Shugaban Sa’ido Akan Nukiliya Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • PDP Ta Tsayar da Goodluck Jonathan Takarar Shugaban Kasa
  • Hawan Gidan Gwamnati A Jihar Gombe
  • Hawan Babbar Sallah A Masarautar Kaltungo Dake Jihar Gombe
  • Sarkin Gombe Ya Yabi Nasarorin Inuwa Yahaya A Fannonin Tsaro Da Raya Kasa
  • Tinubu Ya Jaddada Aniyar Rage Tsadar Rayuwa Da Samar da Ayyukan Yi

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Kasar Faransa Ta Karyata Cire Afirka Ta Kudu Daga G7 Afrika
  • Amurka Zata Saidawa Saudiyya Da Jirgin Yaki Samfurin F35 Labarai
  • Jirgin Dakon Iskar Gas Daga Rasha Ya Sake Hanya Afrika
  • An Kama Maharan Bom Din Maiduguri Tsaro
  • Bahagon Mancha Ya Buge Bahagon Maitakwasara Da Wasun Su! Nishadi
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe Afrika
  • Kasar Colombia Tare Da Amurka Zasu Fitar Da Man Venezuela Labarai
  • APC Ta Bayyana Abba Yusuf A Matsayin Halastaccen Ɗan Takara Bayan Cika Sharudda Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.