Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama Afrika
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara Afrika
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe Afrika
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro Afrika
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa Afrika

Shugaban Kasar Iran Ya Bayyana Samun Sakamako Mai Kyau A Tattaunawa Da Amurka
Published: February 25, 2026 at 5:19 PM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: February 25, 2026

Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian ya bayyana cewa, kasar Iran na ganin daman samun sakamako mai kyau daga zagaye na uku na tattaunawa da Amurka, a ranar Laraba, yayin da wata tawaga ta tashi zuwa birnin Geneva domin tattaunawa kan shirin nukiliyar na Tehran.

Wani babban jami’in gwamnatin Amurka ya fada a ranar Litinin cewa manzon Amurka Steve Witkoff da surukin shugaban Amurka Donald Trump Jared Kushner na shirin ganawa da tawagar Iran karkashin jagorancin ministan harkokin wajen kasar Abbas Araqchi a Geneva ranar Alhamis.

A farkon wannan wata ne kasashen biyu suka koma tattaunawa kan shirin nukiliyar da aka dade ana takaddama a kai, a daidai lokacin da Amurka ke kara karfafa karfin soji a yankin gabas ta tsakiya, gabanin kai hare-hare kan Jamhuriyar Musulunci ta Iran. Iran ta yi barazanar kai hari kan sansanonin Amurka da ke yankin idan aka kai mata hari.

Trump a ranar 19 ga Fabrairu ya ce yana ba Tehran kusan kwanaki 10 zuwa 15 don yin yarjejeniya.

Amurka, Labarai, Sauran Duniya

Post navigation

Previous Post: Shugaba Trump Yace Bazai Bari Iran Ta Mallaki Nukiliya Ba
Next Post: Fafaroma Leo Zai Ziyarci Kasashen Afirka

Karin Labarai Masu Alaka

MDD: Fiye Da Farar Hula Metan 200 Suka Mutu A Sudan Afrika
Dan Gudun Hijira Tarique Rahman Ya Kusa Zama Shugaban Kasa Labarai
Shugaba Tinubu Zai Kara Karbo Bashin Dala Miliyan 516 Afrika
Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama Afrika
Kenya Ta Cimma Yarjejeniya Da Kasar Rasha Afrika
Ukraine Da Syria Zasuyi Haɗin Gwiwar Tsaro Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Anyi Sallar Rokon Ruwa A Saudiya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Jam’iyyu Shida Sun Shiga Zaben Kananan Hukumomin Gombe – GOSIEC Afrika
  • Mourinho Ya ƙara Ta’azzara Takaddamarsa Da Hukumomin ƙwallon ƙafar Turkiyya Wasanni
  • Jama’ar Kasar Iran Sun Bayyana Goyon Baya Ga Ayatollah Mojtaba Khameni Afrika
  • ‘Yan Ta’adda Sun Hallaka Sojoji Da Fararen Hula A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • Shugaba Trump Yace Babu Maganar Kawo Karshen Yakin Amurka Da Iran Amurka
  • Nan Gaba Kadan Kwallon Badminton Zata Samu Karbuwa Kamar Kwallon Kafa A Duniya Labarai
  • Muna Kira Ga Kasashen Duniya Su Sa Baki Don A Saki Mohamed Bazoum Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.